< Psalms 87 >

1 A Psalm of the sons of Korah; a Song. His foundation is in the holy mountains.
Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
2 The LORD loveth the gates of Zion more than all the dwellings of Jacob.
Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
3 Glorious things are spoken of Thee, O city of God. (Selah)
Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
4 'I will make mention of Rahab and Babylon as among them that know Me; behold Philistia, and Tyre, with Ethiopia; this one was born there.'
“Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
5 But of Zion it shall be said: 'This man and that was born in her; and the Most High Himself doth establish her.'
Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
6 The LORD shall count in the register of the peoples: 'This one was born there.' (Selah)
Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
7 And whether they sing or dance, all my thoughts are in Thee.
Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”

< Psalms 87 >