< Psalms 83 >
1 A Song, a Psalm of Asaph. O God, keep not Thou silence; hold not Thy peace, and be not still, O God.
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For, lo, Thine enemies are in an uproar; and they that hate Thee have lifted up the head.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 They hold crafty converse against Thy people, and take counsel against Thy treasured ones.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 They have said: 'Come, and let us cut them off from being a nation; that the name of Israel may be no more in remembrance.'
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 For they have consulted together with one consent; against Thee do they make a covenant;
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 The tents of Edom and the Ishmaelites; Moab, and the Hagrites;
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal, and Ammon, and Amalek; Philistia with the inhabitants of Tyre;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Assyria also is joined with them; they have been an arm to the children of Lot. (Selah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Do Thou unto them as unto Midian; as to Sisera, as to Jabin, at the brook Kishon;
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Who were destroyed at En-dor; they became as dung for the earth.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their nobles like Oreb and Zeeb, and like Zebah and Zalmunna all their princes;
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Who said: 'Let us take to ourselves in possession the habitations of God.'
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 O my God, make them like the whirling dust; as stubble before the wind.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 As the fire that burneth the forest, and as the flame that setteth the mountains ablaze;
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 So pursue them with Thy tempest, and affright them with Thy storm.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Fill their faces with shame; that they may seek Thy name, O LORD.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Let them be ashamed and affrighted for ever; yea, let them be abashed and perish;
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 That they may know that it is Thou alone whose name is the LORD, the Most High over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.