< Psalms 81 >

1 For the Leader; upon the Gittith. A Psalm of Asaph. Sing aloud unto God our strength; shout unto the God of Jacob.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Take up the melody, and sound the timbrel, the sweet harp with the psaltery.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Blow the horn at the new moon, at the full moon for our feast-day.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 For it is a statute for Israel, an ordinance of the God of Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 He appointed it in Joseph for a testimony, when He went forth against the land of Egypt. The speech of one that I knew not did I hear:
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 'I removed his shoulder from the burden; His hands were freed from the basket.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 Thou didst call in trouble, and I rescued thee; I answered thee in the secret place of thunder; I proved thee at the waters of Meribah. (Selah)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Hear, O My people, and I will admonish thee: O Israel, if thou wouldest hearken unto Me!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 There shall no strange god be in thee; neither shalt thou worship any foreign god.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 I am the LORD thy God, who brought thee up out of the land of Egypt; open thy mouth wide, and I will fill it.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 But My people hearkened not to My voice; and Israel would none of Me.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 So I let them go after the stubbornness of their heart, that they might walk in their own counsels.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 Oh that My people would hearken unto Me, that Israel would walk in My ways!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 I would soon subdue their enemies, and turn My hand against their adversaries.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 The haters of the LORD should dwindle away before Him; and their punishment should endure for ever.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 They should also be fed with the fat of wheat; and with honey out of the rock would I satisfy thee.'
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Psalms 81 >