< Psalms 74 >
1 Maschil of Asaph. Why, O God, hast Thou cast us off for ever? Why doth Thine anger smoke against the flock of Thy pasture?
Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
2 Remember Thy congregation, which Thou hast gotten of old, which Thou hast redeemed to be the tribe of Thine inheritance; and mount Zion, wherein Thou hast dwelt.
Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
3 Lift up Thy steps because of the perpetual ruins, even all the evil that the enemy hath done in the sanctuary.
Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
4 Thine adversaries have roared in the midst of Thy meeting-place; they have set up their own signs for signs.
Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
5 It seemed as when men wield upwards axes in a thicket of trees.
Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
6 And now all the carved work thereof together they strike down with hatchet and hammers.
Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
7 They have set Thy sanctuary on fire; they have profaned the dwelling-place of Thy name even to the ground.
Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
8 They said in their heart: 'Let us make havoc of them altogether'; they have burned up all the meeting-places of God in the land.
Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
9 We see not our signs; there is no more any prophet; neither is there among us any that knoweth how long.
Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
10 How long, O God, shall the adversary reproach? Shall the enemy blaspheme Thy name for ever?
Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
11 Why withdrawest Thou Thy hand, even Thy right hand? Draw it out of Thy bosom and consume them.
Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
12 Yet God is my King of old, working salvation in the midst of the earth.
Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
13 Thou didst break the sea in pieces by Thy strength; Thou didst shatter the heads of the sea-monsters in the waters.
Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
14 Thou didst crush the heads of leviathan, Thou gavest him to be food to the folk inhabiting the wilderness.
Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
15 Thou didst cleave fountain and brook; Thou driedst up ever-flowing rivers.
Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
16 Thine is the day, Thine also the night; Thou hast established luminary and sun.
Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
17 Thou hast set all the borders of the earth; Thou hast made summer and winter.
Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
18 Remember this, how the enemy hath reproached the LORD, and how a base people have blasphemed Thy name.
Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
19 O deliver not the soul of Thy turtle-dove unto the wild beast; forget not the life of Thy poor for ever.
Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
20 Look upon the covenant; for the dark places of the land are full of the habitations of violence.
Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
21 O let not the oppressed turn back in confusion; let the poor and needy praise Thy name.
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
22 Arise, O God, plead Thine own cause; remember Thy reproach all the day at the hand of the base man.
Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
23 Forget not the voice of Thine adversaries, the tumult of those that rise up against Thee which ascendeth continually.
Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.