< Psalms 73 >

1 BOOK III A Psalm of Asaph. Surely God is good to Israel, even to such as are pure in heart.
Zabura ta Asaf. Tabbatacce Allah mai alheri ne ga Isra’ila, ga waɗanda suke masu tsabta a zuciya.
2 But as for me, my feet were almost gone; my steps had well nigh slipped.
Amma game da ni, ƙafafuna suna gab da yin santsi; tafin ƙafana ya yi kusan zamewa.
3 For I was envious at the arrogant, when I saw the prosperity of the wicked.
Gama na yi kishin masu girman kai sa’ad da na ga cin gaban da masu mugunta suke yi.
4 For there are no pangs at their death, and their body is sound.
Ba sa yin wata fama; jikunansu lafiya suke da kuma ƙarfi.
5 In the trouble of man they are not; neither are they plagued like men.
Ba sa shan wata wahalar da sauran mutane ke sha; ba su da damuwa irin na’yan adam.
6 Therefore pride is as a chain about their neck; violence covereth them as a garment.
Saboda girman kai ya zama musu abin wuya; tā da hankali ya zama musu riga.
7 Their eyes stand forth from fatness; they are gone beyond the imaginations of their heart.
Daga mugayen zukatansu laifi kan fito mugaye ƙulle-ƙullen da suke cikin zukatansu ba su da iyaka.
8 They scoff, and in wickedness utter oppression; they speak as if there were none on high.
Suna ba’a, suna faɗin mugayen abubuwa; cikin girman kan suna barazana yin danniya.
9 They have set their mouth against the heavens, and their tongue walketh through the earth.
Bakunansu na cewa sama na su ne, kuma harsunansu sun mallaki duniya.
10 Therefore His people return hither; and waters of fullness are drained out by them.
Saboda haka mutanensu sun juya gare su suna kuma shan ruwa a yalwace.
11 And they say: 'How doth God know? And is there knowledge in the Most High?'
Suna cewa, “Yaya Allah zai sani? Mafi Ɗaukaka yana da sani ne?”
12 Behold, such are the wicked; and they that are always at ease increase riches.
Ga yadda mugaye suke, kullum ba su da damuwa, arzikinsu yana ta ƙaruwa.
13 Surely in vain have I cleansed my heart, and washed my hands in innocency;
Tabbatacce a banza na bar zuciyata da tsabta; a banza na wanke hannuwa don nuna rashin laifi.
14 For all the day have I been plagued, and my chastisement came every morning.
Dukan yini na sha annoba; an hukunta ni kowace safiya.
15 If I had said: 'I will speak thus', behold, I had been faithless to the generation of Thy children.
Da na ce, “Zan faɗa haka,” da na bashe’ya’yanka.
16 And when I pondered how I might know this, it was wearisome in mine eyes;
Sa’ad da na yi ƙoƙari in gane wannan, sai ya zama danniya a gare ni
17 Until I entered into the sanctuary of God, and considered their end.
sai da na shiga wuri mai tsarki na Allah; sa’an nan na gane abin da ƙarshensu zai zama.
18 Surely Thou settest them in slippery places; Thou hurlest them down to utter ruin.
Tabbatacce ka sa su a ƙasa mai santsi; ka jefar da su ga hallaka.
19 How are they become a desolation in a moment! They are wholly consumed by terrors.
Duba yadda suka hallaka farat ɗaya, razana ta share su gaba ɗaya!
20 As a dream when one awaketh, so, O Lord, when Thou arousest Thyself, Thou wilt despise their semblance.
Kamar yadda mafarki yake sa’ad da mutum ya farka, haka yake sa’ad da ka farka, ya Ubangiji, za ka rena su kamar almarai.
21 For my heart was in a ferment, and I was pricked in my reins.
Sa’ad da zuciyata ta ɓaci hankalina kuma ya tashi,
22 But I was brutish, and ignorant; I was as a beast before Thee.
na zama marar azanci da jahili; na zama kamar dabba a gabanka.
23 Nevertheless I am continually with Thee; Thou holdest my right hand.
Duk da haka kullum ina tare da kai; ka riƙe ni a hannun damana.
24 Thou wilt guide me with Thy counsel, and afterward receive me with glory.
Ka bishe ni da shawararka, bayan haka kuma za ka kai ni cikin ɗaukaka.
25 Whom have I in heaven but Thee? And beside Thee I desire none upon earth.
Wa nake da shi a sama in ba kai ba? Ba na kuma sha’awar kome a duniya in ban da kai.
26 My flesh and my heart faileth; but God is the rock of my heart and my portion for ever.
Jikina da zuciyata za su iya raunana, amma Allah ne ƙarfin zuciyata da kuma rabona har abada.
27 For, lo, they that go far from Thee shall perish; Thou dost destroy all them that go astray from Thee.
Waɗanda suke nesa da kai za su hallaka; kakan hallaka dukan waɗanda suke maka rashin aminci.
28 But as for me, the nearness of God is my good; I have made the Lord GOD my refuge, that I may tell of all Thy works.
Amma game da ni, yana da kyau in kasance kusa da Allah. Na mai da Ubangiji Mai Iko Duka mafakata; zan yi shelar dukan ayyukanka.

< Psalms 73 >