< Psalms 59 >

1 For the Leader; Al-tashheth. A Psalm of David; Michtam; when Saul sent, and they watched the house to kill him. Deliver me from mine enemies, O my God; set me on high from them that rise up against me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Deliver me from the workers of iniquity, and save me from the men of blood.
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 For, lo, they lie in wait for my soul; the impudent gather themselves together against me; not for my transgression, nor for my sin, O LORD.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 Without my fault, they run and prepare themselves; awake Thou to help me, and behold.
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 Thou therefore, O LORD God of hosts, the God of Israel, arouse Thyself to punish all the nations; show no mercy to any iniquitous traitors. (Selah)
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 They return at evening, they howl like a dog, and go round about the city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Behold, they belch out with their mouth; swords are in their lips: 'For who doth hear?'
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 But Thou, O LORD, shalt laugh at them; Thou shalt have all the nations in derision.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Because of his strength, I will wait for Thee; for God is my high tower.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 The God of my mercy will come to meet me; God will let me gaze upon mine adversaries.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 Slay them not, lest my people forget, make them wander to and fro by Thy power, and bring them down, O Lord our shield.
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 For the sin of their mouth, and the words of their lips, let them even be taken in their pride, and for cursing and lying which they speak.
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Consume them in wrath, consume them, that they be no more; and let them know that God ruleth in Jacob, unto the ends of the earth. (Selah)
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 And they return at evening, they howl like a dog, and go round about the city;
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 They wander up and down to devour, and tarry all night if they have not their fill.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 But as for me, I will sing of Thy strength; yea, I will sing aloud of Thy mercy in the morning; for Thou hast been my high tower, and a refuge in the day of my distress.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 O my strength, unto Thee will I sing praises; for God is my high tower, the God of my mercy.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.

< Psalms 59 >