< Psalms 22 >
1 For the Leader; upon Aijeleth ha-Shahar. A Psalm of David. My God, my God, why hast Thou forsaken me, and art far from my help at the words of my cry?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 O my God, I call by day, but Thou answerest not; and at night, and there is no surcease for me.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Yet Thou art holy, O Thou that art enthroned upon the praises of Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 In Thee did our fathers trust; they trusted, and Thou didst deliver them.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Unto Thee they cried, and escaped; in Thee did they trust, and were not ashamed.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 But I am a worm, and no man; a reproach of men, and despised of the people.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 All they that see me laugh me to scorn; they shoot out the lip, they shake the head:
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 'Let him commit himself unto the LORD! let Him rescue him; let Him deliver him, seeing He delighteth in him.'
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 For Thou art He that took me out of the womb; Thou madest me trust when I was upon my mother's breasts.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Upon Thee I have been cast from my birth; Thou art my God from my mother's womb.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Be not far from me; for trouble is near; for there is none to help.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Many bulls have encompassed me; strong bulls of Bashan have beset me round.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 They open wide their mouth against me, as a ravening and a roaring lion.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 I am poured out like water, and all my bones are out of joint; my heart is become like wax; it is melted in mine inmost parts.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 My strength is dried up like a potsherd; and my tongue cleaveth to my throat; and Thou layest me in the dust of death.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 For dogs have encompassed me; a company of evil-doers have inclosed me; like a lion, they are at my hands and my feet.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 I may count all my bones; they look and gloat over me.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 They part my garments among them, and for my vesture do they cast lots.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 But Thou, O LORD, be not far off; O Thou my strength, hasten to help me.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Deliver my soul from the sword; mine only one from the power of the dog.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Save me from the lion's mouth; yea, from the horns of the wild-oxen do Thou answer me.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 I will declare Thy name unto my brethren; in the midst of the congregation will I praise Thee.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 'Ye that fear the LORD, praise Him; all ye the seed of Jacob, glorify Him; and stand in awe of Him, all ye the seed of Israel.
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 For He hath not despised nor abhorred the lowliness of the poor; neither hath He hid His face from him; but when he cried unto Him, He heard.'
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 From Thee cometh my praise in the great congregation; I will pay my vows before them that fear Him.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Let the humble eat and be satisfied; let them praise the LORD that seek after Him; may your heart be quickened for ever!
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 All the ends of the earth shall remember and turn unto the LORD; and all the kindreds of the nations shall worship before Thee.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 For the kingdom is the LORD'S; and He is the ruler over the nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 All the fat ones of the earth shall eat and worship; all they that go down to the dust shall kneel before Him, even he that cannot keep his soul alive.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 A seed shall serve him; it shall be told of the Lord unto the next generation.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 They shall come and shall declare His righteousness unto a people that shall be born, that He hath done it.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.