< Psalms 135 >
1 Hallelujah. Praise ye the name of the LORD; give praise, O ye servants of the LORD,
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Ye that stand in the house of the LORD, in the courts of the house of our God.
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Praise ye the LORD, for the LORD is good; sing praises unto His name, for it is pleasant.
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 For the LORD hath chosen Jacob unto Himself, and Israel for His own treasure.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 For I know that the LORD is great, and that our Lord is above all gods.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Whatsoever the LORD pleased, that hath He done, in heaven and in earth, in the seas and in all deeps;
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 Who causeth the vapours to ascend from the ends of the earth; He maketh lightnings for the rain; He bringeth forth the wind out of His treasuries.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 Who smote the first-born of Egypt, both of man and beast.
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 He sent signs and wonders into the midst of thee, O Egypt, upon Pharaoh, and upon all his servants.
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 Who smote many nations, and slew mighty kings:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihon king of the Amorites, and Og king of Bashan, and all the kingdoms of Canaan;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 And gave their land for a heritage, a heritage unto Israel His people.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 O LORD, Thy name endureth for ever; thy memorial, O LORD, throughout all generations.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 For the LORD will judge His people, and repent Himself for His servants.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 The idols of the nations are silver and gold, the work of men's hands.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 They have mouths, but they speak not; eyes have they, but they see not;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 They have ears, but they hear not; neither is there any breath in their mouths.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 They that make them shall be like unto them; yea, every one that trusteth in them.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 O house of Israel, bless ye the LORD; O house of Aaron, bless ye the LORD;
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 O house of Levi, bless ye the LORD; ye that fear the LORD, bless ye the LORD.
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Blessed be the LORD out of Zion, who dwelleth at Jerusalem. Hallelujah.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.