< Psalms 122 >
1 A Song of Ascents; of David. I rejoiced when they said unto me: 'Let us go unto the house of the LORD.'
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Our feet are standing within thy gates, O Jerusalem;
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem, that art builded as a city that is compact together;
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 Whither the tribes went up, even the tribes of the LORD, as a testimony unto Israel, to give thanks unto the name of the LORD.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 For there were set thrones for judgment, the thrones of the house of David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Pray for the peace of Jerusalem; may they prosper that love thee.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Peace be within thy walls, and prosperity within thy palaces.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 For my brethren and companions' sakes, I will now say: 'Peace be within thee.'
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 For the sake of the house of the LORD our God I will seek thy good.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.