< Psalms 121 >
1 A Song of Ascents. I will lift up mine eyes unto the mountains: from whence shall my help come?
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2 My help cometh from the LORD, who made heaven and earth.
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3 He will not suffer thy foot to be moved; He that keepeth thee will not slumber.
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4 Behold, He that keepeth Israel doth neither slumber nor sleep.
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5 The LORD is thy keeper; the LORD is thy shade upon thy right hand.
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6 The sun shall not smite thee by day, nor the moon by night.
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
7 The LORD shall keep thee from all evil; He shall keep thy soul.
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8 The LORD shall guard thy going out and thy coming in, from this time forth and for ever.
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.