< Psalms 110 >
1 A Psalm of David. The LORD saith unto my lord: 'Sit thou at My right hand, until I make thine enemies thy footstool.'
Ta Dawuda. Zabura ce. Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”
2 The rod of Thy strength the LORD will send out of Zion: 'Rule thou in the midst of thine enemies.'
Ubangiji zai fadada ikon sandan mulkinka daga Sihiyona za ka yi mulki a tsakiyar abokan gābanka.
3 Thy people offer themselves willingly in the day of thy warfare; in adornments of holiness, from the womb of the dawn, thine is the dew of thy youth.
Rundunarka za su so yin yaƙi a ranarka ta yaƙi. Saye cikin ɗaukaka mai tsarki, daga cikin ciki na safiya za ka karɓi raɓar ƙuruciyarka.
4 The LORD hath sworn, and will not repent: 'Thou art a priest for ever after the manner of Melchizedek.'
Ubangiji ya rantse ba zai kuma canja zuciyarsa ba, “Kai firist ne har abada, bisa ga tsarin Melkizedek.”
5 The Lord at thy right hand doth crush kings in the day of His wrath.
Ubangiji yana a hannun damanka; zai murƙushe sarakuna a ranar fushinsa.
6 He will judge among the nations; He filleth it with dead bodies, He crusheth the head over a wide land.
Zai hukunta al’ummai, yana tarawa gawawwaki yana kuma murƙushe masu mulkin dukan duniya.
7 He will drink of the brook in the way; therefore will he lift up the head.
Zai sha daga rafin da yake kusa da hanya; saboda haka zai ɗaga kansa sama.