< Psalms 108 >

1 A Song, a Psalm of David. My heart is steadfast, O God; I will sing, yea, I will sing praises, even with my glory.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Awake, psaltery and harp; I will awake the dawn.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 I will give thanks unto Thee, O LORD, among the peoples; and I will sing praises unto Thee among the nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 For Thy mercy is great above the heavens, and Thy truth reacheth unto the skies.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Be Thou exalted, O God, above the heavens; and Thy glory be above all the earth.
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 That Thy beloved may be delivered, save with Thy right hand, and answer me.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 God spoke in His holiness, that I would exult; that I would divide Shechem, and mete out the valley of Succoth.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Gilead is mine, Manasseh is mine; Ephraim also is the defence of my head; Judah is my sceptre.
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab is my washpot; upon Edom do I cast my shoe; over Philistia do I cry aloud.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Who will bring me into the fortified city? Who will lead me unto Edom?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Hast not Thou cast us off, O God? and Thou goest not forth, O God, with our hosts?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Give us help against the adversary; for vain is the help of man.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 Through God we shall do valiantly; for He it is that will tread down our adversaries.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.

< Psalms 108 >