< Psalms 104 >

1 Bless the LORD, O my soul. O LORD my God, Thou art very great; Thou art clothed with glory and majesty.
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2 Who coverest Thyself with light as with a garment, who stretchest out the heavens like a curtain;
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3 Who layest the beams of Thine upper chambers in the waters, who makest the clouds Thy chariot, who walkest upon the wings of the wind;
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4 Who makest winds Thy messengers, the flaming fire Thy ministers.
Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5 Who didst establish the earth upon its foundations, that it should not be moved for ever and ever;
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6 Thou didst cover it with the deep as with a vesture; the waters stood above the mountains.
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7 At Thy rebuke they fled, at the voice of Thy thunder they hasted away —
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8 The mountains rose, the valleys sank down — unto the place which Thou hadst founded for them;
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9 Thou didst set a bound which they should not pass over, that they might not return to cover the earth.
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
10 Who sendest forth springs into the valleys; they run between the mountains;
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11 They give drink to every beast of the field, the wild asses quench their thirst.
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12 Beside them dwell the fowl of the heaven, from among the branches they sing.
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13 Who waterest the mountains from Thine upper chambers; the earth is full of the fruit of Thy works.
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14 Who causeth the grass to spring up for the cattle, and herb for the service of man; to bring forth bread out of the earth,
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15 And wine that maketh glad the heart of man, making the face brighter than oil, and bread that stayeth man's heart.
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16 The trees of the LORD have their fill, the cedars of Lebanon, which He hath planted;
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17 Wherein the birds make their nests; as for the stork, the fir-trees are her house.
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18 The high mountains are for the wild goats; the rocks are a refuge for the conies.
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19 Who appointedst the moon for seasons; the sun knoweth his going down.
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20 Thou makest darkness, and it is night, wherein all the beasts of the forest do creep forth.
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21 The young lions roar after their prey, and seek their food from God.
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22 The sun ariseth, they slink away, and couch in their dens.
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23 Man goeth forth unto his work and to his labour until the evening.
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
24 How manifold are Thy works, O LORD! In wisdom hast Thou made them all; the earth is full of Thy creatures.
Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
25 Yonder sea, great and wide, therein are creeping things innumerable, living creatures, both small and great.
Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
26 There go the ships; there is leviathan, whom Thou hast formed to sport therein.
A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
27 All of them wait for Thee, that Thou mayest give them their food in due season.
Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
28 Thou givest it unto them, they gather it; Thou openest Thy hand, they are satisfied with good.
Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
29 Thou hidest Thy face, they vanish; Thou withdrawest their breath, they perish, and return to their dust.
Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
30 Thou sendest forth Thy spirit, they are created; and Thou renewest the face of the earth.
Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
31 May the glory of the LORD endure for ever; let the LORD rejoice in His works!
Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
32 Who looketh on the earth, and it trembleth; He toucheth the mountains, and they smoke.
shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
33 I will sing unto the LORD as long as I live; I will sing praise to my God while I have any being.
Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
34 Let my musing be sweet unto Him; as for me, I will rejoice in the LORD.
Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
35 Let sinners cease out of the earth, and let the wicked be no more. Bless the LORD, O my soul. Hallelujah.
Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.

< Psalms 104 >