< Psalms 101 >
1 A Psalm of David. I will sing of mercy and justice; unto Thee, O LORD, will I sing praises.
Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
2 I will give heed unto the way of integrity; Oh when wilt Thou come unto me? I will walk within my house in the integrity of my heart.
Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
3 I will set no base thing before mine eyes; I hate the doing of things crooked; it shall not cleave unto me.
Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
4 A perverse heart shall depart from me; I will know no evil thing.
Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
5 Whoso slandereth his neighbour in secret, him will I destroy; whoso is haughty of eye and proud of heart, him will I not suffer.
Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
6 Mine eyes are upon the faithful of the land, that they may dwell with me; he that walketh in a way of integrity, he shall minister unto me.
Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
7 He that worketh deceit shall not dwell within my house; he that speaketh falsehood shall not be established before mine eyes.
Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
8 Morning by morning will I destroy all the wicked of the land; to cut off all the workers of iniquity from the city of the LORD.
Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.