< Proverbs 24 >
1 Be not thou envious of evil men, neither desire to be with them.
Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
2 For their heart studieth destruction, and their lips talk of mischief.
gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3 Through wisdom is a house builded; and by understanding it is established;
Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
4 And by knowledge are the chambers filled with all precious and pleasant riches.
ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
5 A wise man is strong; yea, a man of knowledge increaseth strength.
Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
6 For with wise advice thou shalt make thy war; and in the multitude of counsellors there is safety.
don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
7 Wisdom is as unattainable to a fool as corals; he openeth not his mouth in the gate.
Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
8 He that deviseth to do evil, men shall call him a mischievous person.
Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
9 The thought of foolishness is sin; and the scorner is an abomination to men.
Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
10 If thou faint in the day of adversity, thy strength is small indeed.
In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
11 Deliver them that are drawn unto death; and those that are ready to be slain wilt thou forbear to rescue?
Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
12 If thou sayest: 'Behold, we knew not this', doth not He that weigheth the hearts consider it? And He that keepeth thy soul, doth not He know it? And shall not He render to every man according to his works?
In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
13 My son, eat thou honey, for it is good, and the honeycomb is sweet to thy taste;
Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
14 So know thou wisdom to be unto thy soul; if thou hast found it, then shall there be a future, and thy hope shall not be cut off.
Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
15 Lie not in wait, O wicked man, against the dwelling of the righteous, spoil not his resting-place;
Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
16 For a righteous man falleth seven times, and riseth up again, but the wicked stumble under adversity.
gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
17 Rejoice not when thine enemy falleth, and let not thy heart be glad when he stumbleth;
Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
18 Lest the LORD see it, and it displease Him, and He turn away His wrath from him.
in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
19 Fret not thyself because of evildoers, neither be thou envious at the wicked;
Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
20 For there will be no future to the evil man, the lamp of the wicked shall be put out.
gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
21 My son, fear thou the LORD and the king, and meddle not with them that are given to change;
Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
22 For their calamity shall rise suddenly; and who knoweth the ruin from them both?
gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
23 These also are sayings of the wise. To have respect of persons in judgment is not good.
Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
24 He that saith unto the wicked: 'Thou art righteous', peoples shall curse him, nations shall execrate him;
Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
25 But to them that decide justly shall be delight, and a good blessing shall come upon them.
Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
26 He kisseth the lips that giveth a right answer.
Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
27 Prepare thy work without, and make it fit for thyself in the field; and afterwards build thy house.
Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
28 Be not a witness against thy neighbour without cause; and deceive not with thy lips.
Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
29 Say not: 'I will do so to him as he hath done to me; I will render to the man according to his work.'
Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
30 I went by the field of the slothful, and by the vineyard of the man void of understanding;
Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
31 And, lo, it was all grown over with thistles, the face thereof was covered with nettles, and the stone wall thereof was broken down.
ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
32 Then I beheld, and considered well; I saw, and received instruction.
Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
33 'Yet a little sleep, a little slumber, a little folding of the hands to sleep' —
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
34 So shall thy poverty come as a runner, and thy want as an armed man.
sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.