< Proverbs 23 >

1 When thou sittest to eat with a ruler, consider well him that is before thee;
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 And put a knife to thy throat, if thou be a man given to appetite.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Be not desirous of his dainties; seeing they are deceitful food.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Weary not thyself to be rich; cease from thine own wisdom.
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 Wilt thou set thine eyes upon it? it is gone; for riches certainly make themselves wings, like an eagle that flieth toward heaven.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Eat thou not the bread of him that hath an evil eye, neither desire thou his dainties;
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 For as one that hath reckoned within himself, so is he: 'Eat and drink', saith he to thee; but his heart is not with thee.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 The morsel which thou hast eaten shalt thou vomit up, and lose thy sweet words.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 Speak not in the ears of a fool; for he will despise the wisdom of thy words.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Remove not the ancient landmark; and enter not into the fields of the fatherless;
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 For their Redeemer is strong; He will plead their cause with thee.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Apply thy heart unto instruction, and thine ears to the words of knowledge.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Withhold not correction from the child; for though thou beat him with the rod, he will not die.
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 Thou beatest him with the rod, and wilt deliver his soul from the nether-world. (Sheol h7585)
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
15 My son, if thy heart be wise, my heart will be glad, even mine;
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 Yea, my reins will rejoice, when thy lips speak right things.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Let not thy heart envy sinners, but be in the fear of the LORD all the day;
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 For surely there is a future; and thy hope shall not be cut off.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Hear thou, my son, and be wise, and guide thy heart in the way.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Be not among winebibbers; among gluttonous eaters of flesh;
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 For the drunkard and the glutton shall come to poverty; and drowsiness shall clothe a man with rags.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Hearken unto thy father that begot thee, and despise not thy mother when she is old.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Buy the truth, and sell it not; also wisdom, and instruction, and understanding.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 The father of the righteous will greatly rejoice; and he that begetteth a wise child will have joy of him.
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 Let thy father and thy mother be glad, and let her that bore thee rejoice.
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 My son, give me thy heart, and let thine eyes observe my ways.
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 For a harlot is a deep ditch; and an alien woman is a narrow pit.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 She also lieth in wait as a robber, and increaseth the faithless among men.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Who crieth: 'Woe'? who: 'Alas'? who hath contentions? who hath raving? who hath wounds without cause? who hath redness of eyes?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 They that tarry long at the wine; they that go to try mixed wine.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Look not thou upon the wine when it is red, when it giveth its colour in the cup, when it glideth down smoothly;
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 At the last it biteth like a serpent, and stingeth like a basilisk.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Thine eyes shall behold strange things, and thy heart shall utter confused things.
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 Yea, thou shalt be as he that lieth down in the midst of the sea, or as he that lieth upon the top of a mast.
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 'They have struck me, and I felt it not, they have beaten me, and I knew it not; when shall I awake? I will seek it yet again.'
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”

< Proverbs 23 >