< Proverbs 2 >

1 My son, if thou wilt receive my words, and lay up my commandments with thee;
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 So that thou make thine ear attend unto wisdom, and thy heart incline to discernment;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Yea, if thou call for understanding, and lift up thy voice for discernment;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 If thou seek her as silver, and search for her as for hid treasures;
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Then shalt thou understand the fear of the LORD, and find the knowledge of God.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 For the LORD giveth wisdom, out of His mouth cometh knowledge and discernment;
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 He layeth up sound wisdom for the upright, He is a shield to them that walk in integrity;
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 That He may guard the paths of justice, and preserve the way of His godly ones.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Then shalt thou understand righteousness and justice, and equity, yea, every good path.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 For wisdom shall enter into thy heart, and knowledge shall be pleasant unto thy soul;
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Discretion shall watch over thee, discernment shall guard thee;
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 To deliver thee from the way of evil, from the men that speak froward things;
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 Who leave the paths of uprightness, to walk in the ways of darkness;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Who rejoice to do evil, and delight in the frowardness of evil;
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Who are crooked in their ways, and perverse in their paths;
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 To deliver thee from the strange woman, even from the alien woman that maketh smooth her words;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 That forsaketh the lord of her youth, and forgetteth the covenant of her God.
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 For her house sinketh down unto death, and her paths unto the shades;
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 None that go unto her return, neither do they attain unto the paths of life;
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 That thou mayest walk in the way of good men, and keep the paths of the righteous.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 For the upright shall dwell in the land, and the whole-hearted shall remain in it.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 But the wicked shall be cut off from the land, and the faithless shall be plucked up out of it.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Proverbs 2 >