< Proverbs 1 >
1 THE PROVERBS of Solomon the son of David, king of Israel;
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 To know wisdom and instruction; to comprehend the words of understanding;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 To receive the discipline of wisdom, justice, and right, and equity;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 To give prudence to the simple, to the young man knowledge and discretion;
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 That the wise man may hear, and increase in learning, and the man of understanding may attain unto wise counsels;
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 To understand a proverb, and a figure; the words of the wise, and their dark sayings.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 The fear of the LORD is the beginning of knowledge; but the foolish despise wisdom and discipline.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Hear, my son, the instruction of thy father, and forsake not the teaching of thy mother;
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 For they shall be a chaplet of grace unto thy head, and chains about thy neck.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 My son, if sinners entice thee, consent thou not.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 If they say: 'Come with us, let us lie in wait for blood, let us lurk for the innocent without cause;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Let us swallow them up alive as the grave, and whole, as those that go down into the pit; (Sheol )
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
13 We shall find all precious substance, we shall fill our houses with spoil;
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Cast in thy lot among us; let us all have one purse' —
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 My son, walk not thou in the way with them, restrain thy foot from their path;
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 For their feet run to evil, and they make haste to shed blood.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 For in vain the net is spread in the eyes of any bird;
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 And these lie in wait for their own blood, they lurk for their own lives.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 So are the ways of every one that is greedy of gain; it taketh away the life of the owners thereof.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Wisdom crieth aloud in the streets, she uttereth her voice in the broad places;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 She calleth at the head of the noisy streets, at the entrances of the gates, in the city, she uttereth her words:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 'How long, ye thoughtless, will ye love thoughtlessness? And how long will scorners delight them in scorning, and fools hate knowledge?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Turn you at my reproof; behold, I will pour out my spirit unto you, I will make known my words unto you.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Because I have called, and ye refused, I have stretched out my hand, and no man attended,
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 But ye have set at nought all my counsel, and would none of my reproof;
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 I also, in your calamity, will laugh, I will mock when your dread cometh;
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 When your dread cometh as a storm, and your calamity cometh on as a whirlwind; when trouble and distress come upon you.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Then will they call me, but I will not answer, they will seek me earnestly, but they shall not find me.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 For that they hated knowledge, and did not choose the fear of the LORD;
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 They would none of my counsel, they despised all my reproof.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Therefore shall they eat of the fruit of their own way, and be filled with their own devices.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 For the waywardness of the thoughtless shall slay them, and the confidence of fools shall destroy them.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 But whoso hearkeneth unto me shall dwell securely, and shall be quiet without fear of evil.'
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”