< Malachi 4 +

1 For, behold, the day cometh, it burneth as a furnace; and all the proud, and all that work wickedness, shall be stubble; and the day that cometh shall set them ablaze, saith the LORD of hosts, that it shall leave them neither root nor branch.
“Tabbatacce rana tana zuwa; za tă yi ƙuna kamar wutar maƙera. Dukan masu girman kai da kowane mai aikata mugunta zai zama ciyawa, wannan rana mai zuwa za tă ƙone su. Babu saiwa ko reshen da za a bar musu,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
2 But unto you that fear My name shall the sun of righteousness arise with healing in its wings; and ye shall go forth, and gambol as calves of the stall.
Amma ku da kuke girmama sunana, ranar adalci za tă fito tare da warkarwa a fikafikanta. Za ku kuwa fita kuna tsalle kamar’yan maruƙan da aka sake daga garke.
3 And ye shall tread down the wicked; for they shall be ashes under the soles of your feet in the day that I do make, saith the LORD of hosts.
Sa’an nan za ku tattake mugaye; za su zama toka a ƙarƙashin tafin ƙafafunku a ranar da zan aikata waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
4 Remember ye the law of Moses My servant, which I commanded unto him in Horeb for all Israel, even statutes and ordinances.
“Ku tuna da dokar bawana Musa, ƙa’idodi da dokokin da na ba shi a Horeb domin dukan Isra’ila.
5 Behold, I will send you Elijah the prophet before the coming of the great and terrible day of the LORD.
“Ga shi, zan aika muku da annabi Iliya kafin babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji tă zo.
6 And he shall turn the heart of the fathers to the children, and the heart of the children to their fathers; lest I come and smite the land with utter destruction.
Zai juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, zukatan’ya’ya kuma ga iyayensu; in ba haka ba zan bugi ƙasar da hallaka gaba ɗaya.”

< Malachi 4 +