< Lamentations 3 >

1 I am the man that hath seen affliction by the rod of His wrath.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 He hath led me and caused me to walk in darkness and not in light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Surely against me He turneth His hand again and again all the day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 My flesh and my skin hath He worn out; He hath broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He hath builded against me, and compassed me with gall and travail.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 He hath made me to dwell in dark places, as those that have been long dead.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He hath hedged me about, that I cannot go forth; He hath made my chain heavy.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Yea, when I cry and call for help, He shutteth out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He hath enclosed my ways with hewn stone, He hath made my paths crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 He is unto me as a bear lying in wait, as a lion in secret places.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 He hath turned aside my ways, and pulled me in pieces; He hath made me desolate.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He hath bent His bow, and set me as a mark for the arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He hath caused the arrows of His quiver to enter into my reins.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I am become a derision to all my people, and their song all the day.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He hath filled me with bitterness, He hath sated me with wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 He hath also broken my teeth with gravel stones, He hath made me to wallow in ashes.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 And my soul is removed far off from peace, I forgot prosperity.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 And I said: 'My strength is perished, and mine expectation from the LORD.'
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remember mine affliction and mine anguish, the wormwood and the gall.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 My soul hath them still in remembrance, and is bowed down within me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 This I recall to my mind, therefore have I hope.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Surely the LORD'S mercies are not consumed, surely His compassions fail not.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 They are new every morning; great is Thy faithfulness.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 'The LORD is my portion', saith my soul; 'Therefore will I hope in Him.'
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 The LORD is good unto them that wait for Him, to the soul that seeketh Him.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 It is good that a man should quietly wait for the salvation of the LORD.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 It is good for a man that he bear the yoke in his youth.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Let him sit alone and keep silence, because He hath laid it upon him.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Let him put his mouth in the dust, if so be there may be hope.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Let him give his cheek to him that smiteth him, let him be filled full with reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the Lord will not cast off for ever.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 For though He cause grief, yet will He have compassion according to the multitude of His mercies.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 For He doth not afflict willingly, nor grieve the children of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To crush under foot all the prisoners of the earth,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 To turn aside the right of a man before the face of the Most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 To subvert a man in his cause, the Lord approveth not.
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who is he that saith, and it cometh to pass, when the Lord commandeth it not?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Out of the mouth of the Most High proceedeth not evil and good?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Wherefore doth a living man complain, a strong man because of his sins?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Let us search and try our ways, and return to the LORD.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let us lift up our heart with our hands unto God in the heavens.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 We have transgressed and have rebelled; Thou hast not pardoned.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Thou hast covered with anger and pursued us; Thou hast slain unsparingly.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Thou hast covered Thyself with a cloud, so that no prayer can pass through.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Thou hast made us as the offscouring and refuse in the midst of the peoples.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 All our enemies have opened their mouth wide against us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Terror and the pit are come upon us, desolation and destruction.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Mine eye runneth down with rivers of water, for the breach of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Mine eye is poured out, and ceaseth not, without any intermission,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 Till the LORD look forth, and behold from heaven.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mine eye affected my soul, because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 They have chased me sore like a bird, that are mine enemies without cause.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They have cut off my life in the dungeon, and have cast stones upon me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Waters flowed over my head; I said: 'I am cut off.'
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I called upon Thy name, O LORD, Out of the lowest dungeon.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Thou heardest my voice; hide not Thine ear at my sighing, at my cry.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Thou drewest near in the day that I called upon Thee; Thou saidst: 'Fear not.'
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 O Lord, Thou hast pleaded the causes of my soul; Thou hast redeemed my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 O LORD, Thou hast seen my wrong; judge Thou my cause.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Thou hast seen all their vengeance and all their devices against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Thou hast heard their taunt, O LORD, and all their devices against me;
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 The lips of those that rose up against me, and their muttering against me all the day.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Behold Thou their sitting down, and their rising up; I am their song.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Thou wilt render unto them a recompense, O LORD, according to the work of their hands.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Thou wilt give them hardness of heart, Thy curse unto them.
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Thou wilt pursue them in anger, and destroy them from under the heavens of the LORD.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >