< Joshua 5 >
1 And it came to pass, when all the kings of the Amorites, that were beyond the Jordan westward, and all the kings of the Canaanites, that were by the sea, heard how that the LORD had dried up the waters of the Jordan from before the children of Israel, until they were passed over, that their heart melted, neither was there spirit in them any more, because of the children of Israel.
To, da dukan sarakunan Amoriyawa na yammancin Urdun, da dukan sarakunan Kan’aniyawan da suke bakin teku suka ji yadda Ubangiji ya busar da kogin Urdun a gaban Isra’ilawa, har sai da dukansu suka ƙetare, zuciyarsu ta narke, suka karaya sosai har ma suka rasa samun ƙarfin hali su fuskanci Isra’ilawa.
2 At that time the LORD said unto Joshua: 'Make thee knives of flint, and circumcise again the children of Israel the second time.'
A lokacin nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu ka yi wa Isra’ilawa kaciya.”
3 And Joshua made him knives of flint, and circumcised the children of Israel at Gibeath-ha-araloth.
Sai Yoshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa Isra’ilawa kaciya a Gibeyat-Ha’aralot.
4 And this is the cause why Joshua did circumcise: all the people that came forth out of Egypt, that were males, even all the men of war, died in the wilderness by the way, after they came forth out of Egypt.
Dalilin da ya sa ya yi haka shi ne, dukan waɗanda suka fito daga Masar, dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja, sun mutu a cikin jeji a hanya bayan sun bar Masar.
5 For all the people that came out were circumcised; but all the people that were born in the wilderness by the way as they came forth out of Egypt, had not been circumcised.
Dukan mutanen da suka fito daga Masar an yi musu kaciya, amma duk waɗanda aka haifa a jeji a tafiya daga Masar, ba a yi musu ba.
6 For the children of Israel walked forty years in the wilderness, till all the nation, even the men of war that came forth out of Egypt, were consumed, because they hearkened not unto the voice of the LORD; unto whom the LORD swore that He would not let them see the land which the LORD swore unto their fathers that He would give us, a land flowing with milk and honey.
Isra’ilawa sun yi tafiya a jeji shekaru arba’in, har sai da dukan mazan da suka kai shekarun shiga soja da suka bar Masar suka mutu, domin ba su yi wa Ubangiji biyayya ba. Gama Ubangiji ya rantse cewa ba zai bar su su ga ƙasar da ya yi wa iyayensu alkawari da rantsuwa cewa zai ba su ba, ƙasar da zuma da madara suke kwarara, ƙasar da take cike da albarka.
7 And He raised up their children in their stead; them did Joshua circumcise; for they were uncircumcised, because they had not been circumcised by the way.
Sai ya sa yaransu ne suka taso a maimakonsu, su ne waɗanda Yoshuwa ya yi wa kaciya. Sun kasance ba kaciya gama ba a yi musu ba a hanya.
8 And it came to pass, when all the nation were circumcised, every one of them, that they abode in their places in the camp, till they were whole.
Kuma bayan da aka yi wa al’ummar kaciya dukansu, sai suka dakata a nan, sai da suka warke.
9 And the LORD said unto Joshua: 'This day have I rolled away the reproach of Egypt from off you.' Wherefore the name of that place was called Gilgal, unto this day.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Yau na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka ake kiran sunan wurin Gilgal har wa yau.
10 And the children of Israel encamped in Gilgal; and they kept the passover on the fourteenth day of the month at even in the plains of Jericho.
Da yamman rana ta goma sha huɗu ga wata, lokacin da suke a Gilgal a filin Yeriko, Isra’ilawa suka yi Bikin Ƙetarewa.
11 And they did eat of the produce of the land on the morrow after the passover, unleavened cakes and parched corn, in the selfsame day.
A kashegarin Bikin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, burodi marar yisti da hatsin da aka gasa.
12 And the manna ceased on the morrow, after they had eaten of the produce of the land; neither had the children of Israel manna any more; but they did eat of the fruit of the land of Canaan that year.
Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, Manna ta yanke, mutanen Isra’ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan’ana.
13 And it came to pass, when Joshua was by Jericho, that he lifted up his eyes and looked, and, behold, there stood a man over against him with his sword drawn in his hand; and Joshua went unto him, and said unto him: 'Art thou for us, or for our adversaries?'
To, da Yoshuwa ya yi kusa da Yeriko, ya tā da idanunsa ya duba, sai ya ga wani mutum tsaye a gabansa riƙe da takobi, sai Yoshuwa ya je wurinsa ya ce masa, “Kai namu ne ko na abokan gābanmu?”
14 And he said: 'Nay, but I am captain of the host of the LORD; I am now come.' And Joshua fell on his face to the earth, and bowed down, and said unto him: 'What saith my lord unto his servant?'
Mutumin ya ce, “Babu ko ɗaya, na dai zo ne a matsayin shugaban rundunar sojojin Ubangiji.” Sai Yoshuwa ya kwanta da fuskarsa har ƙasa, ya girmama shi, ya ce masa, “Ranka yă daɗe, wane saƙo kake da shi domin bawanka?”
15 And the captain of the LORD'S host said unto Joshua: 'Put off thy shoe from off thy foot; for the place whereon thou standest is holy.' And Joshua did so.
Shugaban rundunar sojojin Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka cire takalmanka, gama wurin da kake tsaye, mai tsarki ne.” Sai Yoshuwa ya cire takalmansa.