< Joshua 16 >
1 And the lot for the children of Joseph went out from the Jordan at Jericho, at the waters of Jericho on the east, going up from Jericho through the hill-country to the wilderness, even to Beth-el.
Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
2 And it went out from Beth-el-luz, and passed along unto the border of the Archites to Ataroth.
Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
3 And it went down westward to the border of the Japhletites, unto the border of Beth-horon the nether, even unto Gezer; and the goings out thereof were at the sea.
ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
4 And the children of Joseph, Manasseh and Ephraim, took their inheritance.
Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
5 And the border of the children of Ephraim according to their families was thus; even the border of their inheritance eastward was Atroth-addar, unto Beth-horon the upper.
Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
6 And the border went out westward, Mich-methath being on the north; and the border turned about eastward unto Taanath-shiloh, and passed along it on the east of Janoah.
ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
7 And it went down from Janoah to Ataroth, and to Naarah, and reached unto Jericho, and went out at the Jordan.
Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
8 From Tappuah the border went along westward to the brook of Kanah; and the goings out thereof were at the sea. This is the inheritance of the tribe of the children of Ephraim according to their families;
Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
9 together with the cities which were separated for the children of Ephraim in the midst of the inheritance of the children of Manasseh, all the cities with their villages.
Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
10 And they drove not out the Canaanites that dwelt in Gezer; but the Canaanites dwelt in the midst of Ephraim, unto this day, and became servants to do taskwork.
Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.