< Joshua 13 >

1 Now Joshua was old and well stricken in years; and the LORD said unto him: 'Thou art old and well stricken in years, and there remaineth yet very much land to be possessed.
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 This is the land that yet remaineth: all the regions of the Philistines, and all the Geshurites;
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 from the Shihor, which is before Egypt, even unto the border of Ekron northward — which is counted to the Canaanites; the five lords of the Philistines: the Gazite, and the Ashdodite, the Ashkelonite, the Gittite, and the Ekronite; also the Avvim
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 on the south; all the land of the Canaanites, and Mearah that belongeth to the Zidonians, unto Aphek, to the border of the Amorites;
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 and the land of the Gebalites, and all Lebanon, toward the sunrising, from Baal-gad under mount Hermon unto the entrance of Hamath;
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 all the inhabitants of the hill-country from Lebanon unto Misrephoth-maim, even all the Zidonians; them will I drive out from before the children of Israel; only allot thou it unto Israel for an inheritance, as I have commanded thee.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 Now therefore divide this land for an inheritance unto the nine tribes, and the half-tribe of Manasseh.'
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 With him the Reubenites and the Gadites received their inheritance, which Moses gave them, beyond the Jordan eastward, even as Moses the servant of the LORD gave them;
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 from Aroer, that is on the edge of the valley of Arnon, and the city that is in the middle of the valley, and all the table-land from Medeba unto Dibon;
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 and all the cities of Sihon king of the Amorites, who reigned in Heshbon, unto the border of the children of Ammon;
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 and Gilead, and the border of the Geshurites and Maacathites, and all mount Hermon, and all Bashan unto Salcah;
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 all the kingdom of Og in Bashan, who reigned in Ashtaroth and in Edrei — the same was left of the remnant of the Rephaim — for these did Moses smite, and drove them out.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 Nevertheless the children of Israel drove not out the Geshurites, nor the Maacathites; but Geshur and Maacath dwelt in the midst of Israel unto this day.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 Only unto the tribe of Levi he gave no inheritance; the offerings of the LORD, the God of Israel, made by fire are his inheritance, as He spoke unto him.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 And Moses gave unto the tribe of the children of Reuben according to their families.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 And their border was from Aroer, that is on the edge of the valley of Arnon, and the city that is in the middle of the valley, and all the table-land by Medeba;
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 Heshbon, and all her cities that are in the table-land; Dibon, and Bamoth-baal, and Beth-baal-meon;
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 and Jahaz, and Kedemoth, and Mephaath;
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 and Kiriathaim, and Sibmah, and Zerethshahar in the mount of the valley;
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 and Beth-peor, and the slopes of Pisgah, and Beth-jeshimoth;
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 and all the cities of the table-land, and all the kingdom of Sihon king of the Amorites, who reigned in Heshbon, whom Moses smote with the chiefs of Midian, Evi, and Rekem, and Zur, and Hur, and Reba, the princes of Sihon, that dwelt in the land.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 Balaam also the son of Beor, the soothsayer, did the children of Israel slay with the sword among the rest of their slain.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 And as for the border of the children of Reuben, the Jordan was their border. This was the inheritance of the children of Reuben according to their families, the cities and the villages thereof.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 And Moses gave unto the tribe of Gad, unto the children of Gad, according to their families.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 And their border was Jazer, and all the cities of Gilead, and half the land of the children of Ammon, unto Aroer that is before Rabbah;
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 and from Heshbon unto Ramath-mizpeh, and Betonim; and from Mahanaim unto the border of Lidbir;
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 and in the valley, Beth-haram, and Beth-nimrah, and Succoth, and Zaphon, the rest of the kingdom of Sihon king of Heshbon, the Jordan being the border thereof, unto the uttermost part of the sea of Chinnereth beyond the Jordan eastward.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 This is the inheritance of the children of Gad according to their families, the cities and the villages thereof.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 And Moses gave inheritance unto the half-tribe of Manasseh; and it was for the half-tribe of the children of Manasseh according to their families.
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 And their border was from Mahanaim, all Bashan, all the kingdom of Og king of Bashan, and all the villages of Jair, which are in Bashan, threescore cities;
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 and half Gilead, and Ashtaroth, and Edrei, the cities of the kingdom of Og in Bashan, were for the children of Machir the son of Manasseh, even for the half of the children of Machir according to their families.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 These are the inheritances which Moses distributed in the plains of Moab, beyond the Jordan at Jericho, eastward.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 But unto the tribe of Levi Moses gave no inheritance; the LORD, the God of Israel, is their inheritance, as He spoke unto them.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Joshua 13 >