< Jonah 2 >

1 Then Jonah prayed unto the LORD his God out of the fish's belly.
Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
2 And he said: I called out of mine affliction unto the LORD, and He answered me; out of the belly of the nether-world cried I, and Thou heardest my voice. (Sheol h7585)
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol h7585)
3 For Thou didst cast me into the depth, in the heart of the seas, and the flood was round about me; all Thy waves and Thy billows passed over me.
Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
4 And I said: 'I am cast out from before Thine eyes'; yet I will look again toward Thy holy temple.
Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
5 The waters compassed me about, even to the soul; the deep was round about me; the weeds were wrapped about my head.
Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
6 I went down to the bottoms of the mountains; the earth with her bars closed upon me for ever; yet hast Thou brought up my life from the pit, O LORD my God.
Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
7 When my soul fainted within me, I remembered the LORD; and my prayer came in unto Thee, into Thy holy temple.
“Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
8 They that regard lying vanities forsake their own mercy.
“Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
9 But I will sacrifice unto Thee with the voice of thanksgiving; that which I have vowed I will pay. Salvation is of the LORD.
Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
10 And the LORD spoke unto the fish, and it vomited out Jonah upon the dry land.
Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.

< Jonah 2 >