< Job 36 >
1 Elihu also proceeded, and said:
Elihu ya ci gaba,
2 Suffer me a little, and I will tell thee; for there are yet words on God's behalf.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I will fetch my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Maker.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 For truly my words are not false; one that is upright in mind is with thee.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Behold, God is mighty, yet He despiseth not any; He is mighty in strength of understanding.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 He preserveth not the life of the wicked; but giveth to the poor their right.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He withdraweth not His eyes from the righteous; but with kings upon the throne He setteth them for ever, and they are exalted.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 And if they be bound in fetters, and be holden in cords of affliction;
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Then He declareth unto them their work, and their transgressions, that they have behaved themselves proudly.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 He openeth also their ear to discipline, and commandeth that they return from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they hearken and serve Him, they shall spend their days in prosperity, and their years in pleasures.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 But if they hearken not, they shall perish by the sword, and they shall die without knowledge.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 But they that are godless in heart lay up anger; they cry not for help when He bindeth them.
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Their soul perisheth in youth, and their life as that of the depraved.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 He delivereth the afflicted by His affliction, and openeth their ear by tribulation.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Yea, He hath allured thee out of distress into a broad place, where there is no straitness; and that which is set on thy table is full of fatness;
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 And thou art full of the judgment of the wicked; judgment and justice take hold on them.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 For beware of wrath, lest thou be led away by thy sufficiency; neither let the greatness of the ransom turn thee aside.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Will thy riches avail, that are without stint, or all the forces of thy strength?
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Desire not the night, when peoples are cut off in their place.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Take heed, regard not iniquity; for this hast thou chosen rather than affliction.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Behold, God doeth loftily in His power; who is a teacher like Him?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who hath enjoined Him His way? Or who hath said: 'Thou hast wrought unrighteousness'?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Remember that thou magnify His work, whereof men have sung.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 All men have looked thereon; man beholdeth it afar off.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Behold, God is great, beyond our knowledge; the number of His years is unsearchable.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 For He draweth away the drops of water, which distil rain from His vapour;
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Which the skies pour down and drop upon the multitudes of men.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Yea, can any understand the spreadings of the clouds, the crashings of His pavilion?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Behold, He spreadeth His light upon it; and He covereth the depths of the sea.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 For by these He judgeth the peoples; He giveth food in abundance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 He covereth His hands with the lightning, and giveth it a charge that it strike the mark.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 The noise thereof telleth concerning it, the cattle also concerning the storm that cometh up.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.