< Job 19 >

1 Then Job answered and said:
Sai Ayuba ya amsa,
2 How long will ye vex my soul, and crush me with words?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 These ten times have ye reproached me; ye are not ashamed that ye deal harshly with me.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 And be it indeed that I have erred, mine error remaineth with myself.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 If indeed ye will magnify yourselves against me, and plead against me my reproach;
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Know now that God hath subverted my cause, and hath compassed me with His net.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Behold, I cry out: 'Violence!' but I am not heard; I cry aloud, but there is no justice.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 He hath fenced up my way that I cannot pass, and hath set darkness in my paths.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 He hath stripped me of my glory, and taken the crown from my head.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He hath broken me down on every side, and I am gone; and my hope hath He plucked up like a tree.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 He hath also kindled His wrath against me, and He counteth me unto Him as one of His adversaries.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 His troops come on together, and cast up their way against me, and encamp round about my tent.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 He hath put my brethren far from me, and mine acquaintance are wholly estranged from me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My kinsfolk have failed, and my familiar friends have forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 They that dwell in my house, and my maids, count me for a stranger; I am become an alien in their sight.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 I call unto my servant, and he giveth me no answer, though I entreat him with my mouth.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 My breath is abhorred of my wife, and I am loathsome to the children of my tribe.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 Even urchins despised me; if I arise, they speak against me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 All my intimate friends abhor me; and they whom I loved are turned against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 My bone cleaveth to my skin and to my flesh, and I am escaped with the skin of my teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Have pity upon me, have pity upon me, O ye my friends; for the hand of God hath touched me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why do ye persecute me as God, and are not satisfied with my flesh?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Oh that my words were now written! Oh that they were inscribed in a book!
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 That with an iron pen and lead they were graven in the rock for ever!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 But as for me, I know that my Redeemer liveth, and that He will witness at the last upon the dust;
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 And when after my skin this is destroyed, then without my flesh shall I see God;
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Whom I, even I, shall see for myself, and mine eyes shall behold, and not another's. My reins are consumed within me.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 If ye say: 'How we will persecute him!' seeing that the root of the matter is found in me;
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Be ye afraid of the sword; for wrath bringeth the punishments of the sword, that ye may know there is a judgment.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >