< Job 14 >
1 Man that is born of a woman is of few days, and full of trouble.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 He cometh forth like a flower, and withereth; he fleeth also as a shadow, and continueth not.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 And dost Thou open Thine eyes upon such a one, and bringest me into judgment with Thee?
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Who can bring a clean thing out of an unclean? not one.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Seeing his days are determined, the number of his months is with Thee, and Thou hast appointed his bounds that he cannot pass;
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Look away from him, that he may rest, till he shall accomplish, as a hireling, his day.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 For there is hope of a tree, if it be cut down, that it will sprout again, and that the tender branch thereof will not cease.
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Though the root thereof wax old in the earth, and the stock thereof die in the ground;
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 Yet through the scent of water it will bud, and put forth boughs like a plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 But man dieth, and lieth low; yea, man perisheth, and where is he?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 As the waters fail from the sea, and the river is drained dry;
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 So man lieth down and riseth not; till the heavens be no more, they shall not awake, nor be roused out of their sleep.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 Oh that Thou wouldest hide me in the nether-world, that Thou wouldest keep me secret, until Thy wrath be past, that Thou wouldest appoint me a set time, and remember me! — (Sheol )
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol )
14 If a man die, may he live again? All the days of my service would I wait, till my relief should come —
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 Thou wouldest call, and I would answer Thee; Thou wouldest have a desire to the work of Thy hands.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 But now Thou numberest my steps, Thou dost not even wait for my sin;
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 My transgression is sealed up in a bag, and Thou heapest up mine iniquity.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 And surely the mountain falling crumbleth away, and the rock is removed out of its place;
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 The waters wear the stones; the overflowings thereof wash away the dust of the earth; so Thou destroyest the hope of man.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 Thou prevailest for ever against him, and he passeth; Thou changest his countenance, and sendest him away.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 His sons come to honour, and he knoweth it not; and they are brought low, but he regardeth them not.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 But his flesh grieveth for him, and his soul mourneth over him.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”