< Job 13 >

1 Lo, mine eye hath seen all this, mine ear hath heard and understood it.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 What ye know, do I know also; I am not inferior unto you.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Notwithstanding I would speak to the Almighty, and I desire to reason with God.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 But ye are plasterers of lies, ye are all physicians of no value.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 Oh that ye would altogether hold your peace! and it would be your wisdom.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Hear now my reasoning, and hearken to the pleadings of my lips.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Will ye speak unrighteously for God, and talk deceitfully for Him?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Will ye show Him favour? Will ye contend for God?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Would it be good that He should search you out? Or as one mocketh a man, will ye mock Him?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 He will surely reprove you, if ye do secretly show favour.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Shall not His majesty terrify you, and His dread fall upon you?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Your memorials shall be like unto ashes, your eminences to eminences of clay.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Hold your peace, let me alone, that I may speak, and let come on me what will.
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Wherefore? I will take my flesh in my teeth, and put my life in my hand.
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Though He slay me, yet will I trust in Him; but I will argue my ways before Him.
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 This also shall be my salvation, that a hypocrite cannot come before Him.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Hear diligently my speech, and let my declaration be in your ears.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Behold now, I have ordered my cause; I know that I shall be justified.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Who is he that will contend with me? For then would I hold my peace and die.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Only do not two things unto me, then will I not hide myself from Thee:
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Withdraw Thy hand far from me; and let not Thy terror make me afraid.
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Then call Thou, and I will answer; or let me speak, and answer Thou me.
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 How many are mine iniquities and sins? Make me to know my transgression and my sin.
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Wherefore hidest Thou Thy face, and holdest me for Thine enemy?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Wilt Thou harass a driven leaf? And wilt Thou pursue the dry stubble?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 That Thou shouldest write bitter things against me, and make me to inherit the iniquities of my youth.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Thou puttest my feet also in the stocks, and lookest narrowly unto all my paths; Thou drawest Thee a line about the soles of my feet;
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 Though I am like a wine-skin that consumeth, like a garment that is moth-eaten.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.

< Job 13 >