< Jeremiah 46 >

1 The word of the LORD which came to Jeremiah the prophet concerning the nations.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 Of Egypt: concerning the army of Pharaoh-neco king of Egypt, which was by the river Euphrates in Carchemish, which Nebuchadrezzar king of Babylon smote in the fourth year of Jehoiakim the son of Josiah, king of Judah.
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 Make ready buckler and shield, and draw near to battle.
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Harness the horses, and mount, ye horsemen, and stand forth with your helmets; furbish the spears, put on the coats of mail.
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 Wherefore do I see them dismayed and turned backward? and their mighty ones are beaten down, and they are fled apace, and look not back; terror is on every side, saith the LORD.
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 The swift cannot flee away, nor the mighty man escape; in the north by the river Euphrates have they stumbled and fallen.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 Who is this like the Nile that riseth up, like the rivers whose waters toss themselves?
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 Egypt is like the Nile that riseth up, and like the rivers whose waters toss themselves; and he saith: 'I will rise up, I will cover the earth, I will destroy the city and the inhabitants thereof.'
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 Prance, ye horses, and rush madly, ye chariots; and let the mighty men go forth: Cush and Put, that handle the shield, and the Ludim, that handle and bend the bow.
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 For the Lord GOD of hosts shall have on that day a day of vengeance, that He may avenge Him of His adversaries; and the sword shall devour and be satiate, and shall be made drunk with their blood; for the Lord GOD of hosts hath a sacrifice in the north country by the river Euphrates.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 Go up into Gilead, and take balm, O virgin daughter of Egypt; in vain dost thou use many medicines; there is no cure for thee.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 The nations have heard of thy shame, and the earth is full of thy cry; for the mighty man hath stumbled against the mighty, they are fallen both of them together.
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 The word that the LORD spoke to Jeremiah the prophet, how that Nebuchadrezzar king of Babylon should come and smite the land of Egypt.
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 Declare ye in Egypt, and announce in Migdol, and announce in Noph and in Tahpanhes; say ye: 'Stand forth, and prepare thee, for the sword hath devoured round about thee.'
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Why is thy strong one overthrown? He stood not, because the LORD did thrust him down.
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 He made many to stumble; yea, they fell one upon another, and said: 'Arise, and let us return to our own people, and to the land of our birth, from the oppressing sword.'
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 They cried there: 'Pharaoh king of Egypt is but a noise; he hath let the appointed time pass by.'
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 As I live, saith the King, whose name is the LORD of hosts, surely like Tabor among the mountains, and like Carmel by the sea, so shall he come.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 O thou daughter that dwellest in Egypt, furnish thyself to go into captivity; for Noph shall become a desolation, and shall be laid waste, without inhabitant.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 Egypt is a very fair heifer; but the gadfly out of the north is come, it is come.
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 Also her mercenaries in the midst of her are like calves of the stall, for they also are turned back, they are fled away together, they did not stand; for the day of their calamity is come upon them, the time of their visitation.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 The sound thereof shall go like the serpent's; for they march with an army, and come against her with axes, as hewers of wood.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 They cut down her forest, saith the LORD, though it cannot be searched; because they are more than the locusts, and are innumerable.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 The daughter of Egypt is put to shame; she is delivered into the hand of the people of the north.
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 The LORD of hosts, the God of Israel, saith: Behold, I will punish Amon of No, and Pharaoh, and Egypt, with her gods, and her kings; even Pharaoh, and them that trust in him;
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 and I will deliver them into the hand of those that seek their lives, and into the hand of Nebuchadrezzar king of Babylon, and into the hand of his servants; and afterwards it shall be inhabited, as in the days of old, saith the LORD.
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 But fear not thou, O Jacob My servant, neither be dismayed, O Israel; for, lo, I will save thee from afar, and thy seed from the land of their captivity; and Jacob shall again be quiet and at ease, and none shall make him afraid.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 Fear not thou, O Jacob My servant, saith the LORD, for I am with thee; for I will make a full end of all the nations whither I have driven thee, but I will not make a full end of thee; and I will correct thee in measure, but will not utterly destroy thee.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”

< Jeremiah 46 >