< Jeremiah 33 >
1 Moreover the word of the LORD came unto Jeremiah the second time, while he was yet shut up in the court of the guard, saying:
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
2 Thus saith the LORD the Maker thereof, the LORD that formed it to establish it, the LORD is His name:
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
3 Call unto Me, and I will answer thee, and will tell thee great things, and hidden, which thou knowest not.
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
4 For thus saith the LORD, the God of Israel, concerning the houses of this city, and concerning the houses of the kings of Judah, which are broken down for mounds, and for ramparts;
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
5 whereon they come to fight with the Chaldeans, even to fill them with the dead bodies of men, whom I have slain in Mine anger and in My fury, and for all whose wickedness I have hid My face from this city:
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
6 Behold, I will bring it healing and cure, and I will cure them; and I will reveal unto them the abundance of peace and truth.
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
7 And I will cause the captivity of Judah and the captivity of Israel to return, and will build them, as at the first.
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
8 And I will cleanse them from all their iniquity, whereby they have sinned against Me; and I will pardon all their iniquities, whereby they have sinned against Me, and whereby they have transgressed against Me.
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
9 And this city shall be to Me for a name of joy, for a praise and for a glory, before all the nations of the earth, which shall hear all the good that I do unto them, and shall fear and tremble for all the good and for all the peace that I procure unto it.
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
10 Thus saith the LORD: Yet again there shall be heard in this place, whereof ye say: It is waste, without man and without beast, even in the cities of Judah, and in the streets of Jerusalem, that are desolate, without man and without inhabitant and without beast,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
11 the voice of joy and the voice of gladness, the voice of the bridegroom and the voice of the bride, the voice of them that say: 'Give thanks to the LORD of hosts, for the LORD is good, for His mercy endureth for ever', even of them that bring offerings of thanksgiving into the house of the LORD. For I will cause the captivity of the land to return as at the first, saith the LORD.
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
12 Thus saith the LORD of hosts: Yet again shall there be in this place, which is waste, without man and without beast, and in all the cities thereof, a habitation of shepherds causing their flocks to lie down.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
13 In the cities of the hill-country, in the cities of the Lowland, and in the cities of the South, and in the land of Benjamin, and in the places about Jerusalem, and in the cities of Judah, shall the flocks again pass under the hands of him that counteth them, saith the LORD.
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
14 Behold, the days come, saith the LORD, that I will perform that good word which I have spoken concerning the house of Israel and concerning the house of Judah.
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
15 In those days, and at that time, will I cause a shoot of righteousness to grow up unto David; and he shall execute justice and righteousness in the land.
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
16 In those days shall Judah be saved, and Jerusalem shall dwell safely; and this is the name whereby she shall be called, the LORD is our righteousness.
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
17 For thus saith the LORD: There shall not be cut off unto David a man to sit upon the throne of the house of Israel;
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
18 neither shall there be cut off unto the priests the Levites a man before Me to offer burnt-offerings, and to burn meal-offerings, and to do sacrifice continually.
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
19 And the word of the LORD came unto Jeremiah, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
20 Thus saith the LORD: If ye can break My covenant with the day, and My covenant with the night, so that there should not be day and night in their season;
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
21 Then may also My covenant be broken with David My servant, that he should not have a son to reign upon his throne; and with the Levites the priests, My ministers.
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
22 As the host of heaven cannot be numbered, neither the sand of the sea measured; so will I multiply the seed of David My servant, and the Levites that minister unto Me.
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
23 And the word of the LORD came to Jeremiah, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24 'Considerest thou not what this people have spoken, saying: The two families which the LORD did choose, He hath cast them off? and they contemn My people, that they should be no more a nation before them.
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25 Thus saith the LORD: If My covenant be not with day and night, if I have not appointed the ordinances of heaven and earth;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26 then will I also cast away the seed of Jacob, and of David My servant, so that I will not take of his seed to be rulers over the seed of Abraham, Isaac, and Jacob; for I will cause their captivity to return, and will have compassion on them.'
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”