< Jeremiah 10 >

1 Hear ye the word which the LORD speaketh unto you, O house of Israel;
Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
2 thus saith the LORD: Learn not the way of the nations, and be not dismayed at the signs of heaven; for the nations are dismayed at them.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
3 For the customs of the peoples are vanity; for it is but a tree which one cutteth out of the forest, the work of the hands of the workman with the axe.
Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
4 They deck it with silver and with gold, they fasten it with nails and with hammers, that it move not.
Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
5 They are like a pillar in a garden of cucumbers, and speak not; they must needs be borne, because they cannot go. Be not afraid of them, for they cannot do evil, neither is it in them to do good.
Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
6 There is none like unto Thee, O LORD; Thou art great, and Thy name is great in might.
Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
7 Who would not fear Thee, O king of the nations? For it befitteth Thee; forasmuch as among all the wise men of the nations, and in all their royalty, there is none like unto Thee.
Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
8 But they are altogether brutish and foolish: the vanities by which they are instructed are but a stock;
Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
9 Silver beaten into plates which is brought from Tarshish, and gold from Uphaz, the work of the craftsman and of the hands of the goldsmith; blue and purple is their clothing; they are all the work of skilful men.
An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
10 But the LORD God is the true God, He is the living God, and the everlasting King; at His wrath the earth trembleth, and the nations are not able to abide His indignation.
Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
11 Thus shall ye say unto them: 'The gods that have not made the heavens and the earth, these shall perish from the earth, and from under the heavens.'
“Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
12 He that hath made the earth by His power, that hath established the world by His wisdom, and hath stretched out the heavens by His understanding;
Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
13 At the sound of His giving a multitude of waters in the heavens, when He causeth the vapours to ascend from the ends of the earth; when He maketh lightnings with the rain, and bringeth forth the wind out of His treasuries;
Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
14 Every man is proved to be brutish, without knowledge, every goldsmith is put to shame by the graven image, his molten image is falsehood, and there is no breath in them.
Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
15 They are vanity, a work of delusion; in the time of their visitation they shall perish.
Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
16 Not like these is the portion of Jacob; for He is the former of all things, and Israel is the tribe of His inheritance; the LORD of hosts is His name.
Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
17 Gather up thy wares from the ground, O thou that abidest in the siege.
Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
18 For thus saith the LORD: Behold, I will sling out the inhabitants of the land at this time, and will distress them, that they may feel it.
Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
19 Woe is me for my hurt! My wound is grievous; but I said: 'This is but a sickness, and I must bear it.'
Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
20 My tent is spoiled, and all my cords are broken; my children are gone forth of me, and they are not; there is none to stretch forth my tent any more, and to set up my curtains.
An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
21 For the shepherds are become brutish, and have not inquired of the LORD; therefore they have not prospered, and all their flocks are scattered.
Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
22 Hark! a report, behold, it cometh, and a great commotion out of the north country, to make the cities of Judah desolate, a dwelling-place of jackals.
Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
23 O LORD, I know that man's way is not his own; it is not in man to direct his steps as he walketh.
Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
24 O LORD, correct me, but in measure; not in Thine anger, lest Thou diminish me.
Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
25 Pour out Thy wrath upon the nations that know Thee not, and upon the families that call not on Thy name; for they have devoured Jacob, yea, they have devoured him and consumed him, and have laid waste his habitation.
Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.

< Jeremiah 10 >