< Isaiah 1 >

1 THE VISION of Isaiah the son of Amoz, which he saw concerning Judah and Jerusalem, in the days of Uzziah, Jotham, Ahaz, and Hezekiah, kings of Judah.
Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
2 Hear, O heavens, and give ear, O earth, for the LORD hath spoken: Children I have reared, and brought up, and they have rebelled against Me.
Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
3 The ox knoweth his owner, and the ass his master's crib; but Israel doth not know, My people doth not consider.
Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
4 Ah sinful nation, a people laden with iniquity, a seed of evil-doers, children that deal corruptly; they have forsaken the LORD, they have contemned the Holy One of Israel, they are turned away backward.
Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
5 On what part will ye yet be stricken, seeing ye stray away more and more? The whole head is sick, and the whole heart faint;
Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
6 From the sole of the foot even unto the head there is no soundness in it; but wounds, and bruises, and festering sores: they have not been pressed, neither bound up, neither mollified with oil.
Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
7 Your country is desolate; your cities are burned with fire; your land, strangers devour it in your presence, and it is desolate, as overthrown by floods.
Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
8 And the daughter of Zion is left as a booth in a vineyard, as a lodge in a garden of cucumbers, as a besieged city.
An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
9 Except the LORD of hosts had left unto us a very small remnant, we should have been as Sodom, we should have been like unto Gomorrah.
Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
10 Hear the word of the LORD, ye rulers of Sodom; give ear unto the law of our God, ye people of Gomorrah.
Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
11 To what purpose is the multitude of your sacrifices unto Me? saith the LORD; I am full of the burnt-offerings of rams, and the fat of fed beasts; and I delight not in the blood of bullocks, or of lambs, or of he-goats.
Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
12 When ye come to appear before Me, who hath required this at your hand, to trample My courts?
Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
13 Bring no more vain oblations; it is an offering of abomination unto Me; new moon and sabbath, the holding of convocations — I cannot endure iniquity along with the solemn assembly.
Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
14 Your new moons and your appointed seasons My soul hateth; they are a burden unto Me; I am weary to bear them.
Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
15 And when ye spread forth your hands, I will hide Mine eyes from you; yea, when ye make many prayers, I will not hear; your hands are full of blood.
Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
16 Wash you, make you clean, put away the evil of your doings from before Mine eyes, cease to do evil;
Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
17 Learn to do well; seek justice, relieve the oppressed, judge the fatherless, plead for the widow.
Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
18 Come now, and let us reason together, saith the LORD; though your sins be as scarlet, they shall be as white as snow; though they be red like crimson, they shall be as wool.
Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
19 If ye be willing and obedient, ye shall eat the good of the land;
In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
20 But if ye refuse and rebel, ye shall be devoured with the sword; for the mouth of the LORD hath spoken.
amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
21 How is the faithful city become a harlot! She that was full of justice, righteousness lodged in her, but now murderers.
Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
22 Thy silver is become dross, thy wine mixed with water.
Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
23 Thy princes are rebellious, and companions of thieves; every one loveth bribes, and followeth after rewards; they judge not the fatherless, neither doth the cause of the widow come unto them.
Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
24 Therefore saith the Lord, the LORD of hosts, the Mighty One of Israel: Ah, I will ease Me of Mine adversaries, and avenge Me of Mine enemies;
Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
25 And I will turn My hand upon thee, and purge away thy dross as with lye, and will take away all thine alloy;
Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
26 And I will restore thy judges as at the first, and thy counsellors as at the beginning; afterward thou shalt be called The city of righteousness, the faithful city.
Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
27 Zion shall be redeemed with justice, and they that return of her with righteousness.
Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
28 But the destruction of the transgressors and the sinners shall be together, and they that forsake the LORD shall be consumed.
Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
29 For they shall be ashamed of the terebinths which ye have desired, and ye shall be confounded for the gardens that ye have chosen.
“Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
30 For ye shall be as a terebinth whose leaf fadeth, and as a garden that hath no water.
Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
31 And the strong shall be as tow, and his work as a spark; and they shall both burn together, and none shall quench them.
Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”

< Isaiah 1 >