< Isaiah 32 >

1 Behold, a king shall reign in righteousness, and as for princes, they shall rule in justice.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 And a man shall be as in a hiding-place from the wind, and a covert from the tempest; as by the watercourses in a dry place, as in the shadow of a great rock in a weary land.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 And the eyes of them that see shall not be closed, and the ears of them that hear shall attend.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 The heart also of the rash shall understand knowledge, and the tongue of the stammerers shall be ready to speak plainly.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 The vile person shall be no more called liberal, nor the churl said to be noble.
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 For the vile person will speak villainy, and his heart will work iniquity, to practise ungodliness, and to utter wickedness against the LORD, to make empty the soul of the hungry, and to cause the drink of the thirsty to fail.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 The instruments also of the churl are evil; he deviseth wicked devices to destroy the poor with lying words, and the needy when he speaketh right.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 But the liberal deviseth liberal things; and by liberal things shall he stand.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 Rise up, ye women that are at ease, and hear my voice; ye confident daughters, give ear unto my speech.
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 After a year and days shall ye be troubled, ye confident women; for the vintage shall fail, the ingathering shall not come.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Tremble, ye women that are at ease; be troubled, ye confident ones; strip you, and make you bare, and gird sackcloth upon your loins,
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 Smiting upon the breasts for the pleasant fields, for the fruitful vine;
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 For the land of my people whereon thorns and briers come up; yea, for all the houses of joy and the joyous city.
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 For the palace shall be forsaken; the city with its stir shall be deserted; the mound and the tower shall be for dens for ever, a joy of wild asses, a pasture of flocks;
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 Until the spirit be poured upon us from on high, and the wilderness become a fruitful field, and the fruitful field be counted for a forest.
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 Then justice shall dwell in the wilderness, and righteousness shall abide in the fruitful field.
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 And the work of righteousness shall be peace; and the effect of righteousness quietness and confidence for ever.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 And my people shall abide in a peaceable habitation, and in secure dwellings, and in quiet resting-places.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 And it shall hail, in the downfall of the forest; but the city shall descend into the valley.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Happy are ye that sow beside all waters, that send forth freely the feet of the ox and the ass.
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.

< Isaiah 32 >