< Isaiah 27 >

1 In that day the LORD with His sore and great and strong sword will punish leviathan the slant serpent, and leviathan the tortuous serpent; and He will slay the dragon that is in the sea.
A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
2 In that day sing ye of her: 'A vineyard of foaming wine!'
A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
3 I the LORD do guard it, I water it every moment; lest Mine anger visit it, I guard it night and day.
Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
4 Fury is not in Me; would that I were as the briers and thorns in flame! I would with one step burn it altogether.
Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
5 Or else let him take hold of My strength, that he may make peace with Me; yea, let him make peace with Me.
Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
6 In days to come shall Jacob take root, Israel shall blossom and bud; and the face of the world shall be filled with fruitage.
A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
7 Hath He smitten him as He smote those that smote him? Or is he slain according to the slaughter of them that were slain by Him?
Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
8 In full measure, when Thou sendest her away, Thou dost contend with her; He hath removed her with His rough blast in the day of the east wind.
Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
9 Therefore by this shall the iniquity of Jacob be expiated, and this is all the fruit of taking away his sin: when he maketh all the stones of the altar as chalkstones that are beaten in pieces, so that the Asherim and the sun-images shall rise no more.
A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
10 For the fortified city is solitary, a habitation abandoned and forsaken, like the wilderness; there shall the calf feed, and there shall he lie down, and consume the branches thereof.
Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
11 When the boughs thereof are withered, they shall be broken off; the women shall come, and set them on fire; for it is a people of no understanding; therefore He that made them will not have compassion upon them, and He that formed them will not be gracious unto them.
Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
12 And it shall come to pass in that day, that the LORD will beat off His fruit from the flood of the River unto the Brook of Egypt, and ye shall be gathered one by one, O ye children of Israel.
A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
13 And it shall come to pass in that day, that a great horn shall be blown; and they shall come that were lost in the land of Assyria, and they that were dispersed in the land of Egypt; and they shall worship the LORD in the holy mountain at Jerusalem.
Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.

< Isaiah 27 >