< Isaiah 13 >

1 The burden of Babylon, which Isaiah the son of Amoz did see.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Set ye up an ensign upon the high mountain, lift up the voice unto them, wave the hand, that they may go into the gates of the nobles.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 I have commanded My consecrated ones, yea, I have called My mighty ones for mine anger, even My proudly exulting ones.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Hark, a tumult in the mountains, like as of a great people! Hark, the uproar of the kingdoms of the nations gathered together! The LORD of hosts mustereth the host of the battle.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 They come from a far country, from the end of heaven, even the LORD, and the weapons of His indignation, to destroy the whole earth.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Howl ye; for the day of the LORD is at hand; as destruction from the Almighty shall it come.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 Therefore shall all hands be slack, and every heart of man shall melt.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 And they shall be affrighted; pangs and throes shall take hold of them; they shall be in pain as a woman in travail; they shall look aghast one at another; their faces shall be faces of flame.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Behold, the day of the LORD cometh, cruel, and full of wrath and fierce anger; to make the earth a desolation, and to destroy the sinners thereof out of it,
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 For the stars of heaven and the constellations thereof shall not give their light; the sun shall be darkened in his going forth, and the moon shall not cause her light to shine.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 And I will visit upon the world their evil, and upon the wicked their iniquity; and I will cause the arrogancy of the proud to cease, and will lay low the haughtiness of the tyrants.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 I will make man more rare than fine gold, even man than the pure gold of Ophir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 Therefore I will make the heavens to tremble, and the earth shall be shaken out of her place, for the wrath of the LORD of hosts, and for the day of His fierce anger.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 And it shall come to pass, that as the chased gazelle, and as sheep that no man gathereth, they shall turn every man to his own people, and shall flee every man to his own land.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Every one that is found shall be thrust through; and every one that is caught shall fall by the sword.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Their babes also shall be dashed in pieces before their eyes; their houses shall be spoiled, and their wives ravished.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Behold, I will stir up the Medes against them, who shall not regard silver, and as for gold, they shall not delight in it.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 And their bows shall dash the young men in pieces; and they shall have no pity on the fruit of the womb; their eye shall not spare children.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 And Babylon, the glory of kingdoms, the beauty of the Chaldeans' pride, shall be as when God overthrew Sodom and Gomorrah.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 It shall never be inhabited, neither shall it be dwelt in from generation to generation; neither shall the Arabian pitch tent there; neither shall the shepherds make their fold there.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 But wild-cats shall lie there; and their houses shall be full of ferrets; and ostriches shall dwell there, and satyrs shall dance there.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 And jackals shall howl in their castles, and wild-dogs in the pleasant palaces; and her time is near to come, and her days shall not be prolonged.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaiah 13 >