< Hosea 5 >
1 Hear this, O ye priests, and attend, ye house of Israel, and give ear, O house of the king, for unto you pertaineth the judgment; for ye have been a snare on Mizpah, and a net spread upon Tabor.
“Ku ji wannan, ku firistoci! Ku kasa kunne, ku Isra’ilawa! Ku saurara, ya ku gidan sarauta! Wannan hukunci yana a kanku, kun zama tarko a Mizfa, ragar da aka shimfiɗa a kan Tabor.
2 And they that fall away are gone deep in making slaughter; and I am rejected of them all.
’Yan tawaye sun yi zurfi cikin kisan gilla. Zan hore su duka.
3 I, even I, know Ephraim, and Israel is not hid from Me; for now, O Ephraim, thou hast committed harlotry, Israel is defiled.
Na san Efraim ƙaf; Isra’ila ba a ɓoye take a gare ni ba. Efraim, yanzu ka juya ka shiga karuwanci; Isra’ila ta lalace.
4 Their doings will not suffer them to return unto their God; for the spirit of harlotry is within them, and they know not the LORD.
“Ayyukansu ba su ba su dama su koma ga Allahnsu ba. Halin karuwanci yana cikin zuciyarsu; ba su yarda da Ubangiji ba.
5 But the pride of Israel shall testify to his face; and Israel and Ephraim shall stumble in their iniquity, Judah also shall stumble with them.
Girmankan Isra’ila yana ba da shaida a kansu; Isra’ilawa, har ma Efraim, sun yi tuntuɓe a cikin zunubinsu; Yahuda ma ya yi tuntuɓe tare da su.
6 With their flocks and with their herds they shall go to seek the LORD, but they shall not find Him; He hath withdrawn Himself from them.
Sa’ad da suka tafi tare da garkunan shanu, tumaki da awakinsu don su nemi Ubangiji, ba za su same shi ba; ya janye kansa daga gare su.
7 They have dealt treacherously against the LORD, for they have begotten strange children; now shall the new moon devour them with their portions.
Su marasa aminci ne ga Ubangiji; suna haihuwar shegu. Yanzu bukukkuwar Sabon Watansu za su cinye su da gonakinsu.
8 Blow ye the horn in Gibeah, and the trumpet in Ramah; sound an alarm at Beth-aven: 'Behind thee, O Benjamin!'
“Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
9 Ephraim shall be desolate in the day of rebuke; among the tribes of Israel do I make known that which shall surely be.
Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
10 The princes of Judah are like them that remove the landmark; I will pour out My wrath upon them like water.
Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
11 Oppressed is Ephraim, crushed in his right; because he willingly walked after filth.
An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
12 Therefore am I unto Ephraim as a moth, and to the house of Judah as rottenness.
Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
13 And when Ephraim saw his sickness, and Judah his wound, Ephraim went to Assyria, and sent to King Contentious; but he is not able to heal you, neither shall he cure you of your wound.
“Sa’ad da Efraim ya ga ciwonsa, Yahuda kuwa miyakunta, sai Efraim ya juya ga Assuriya, ya aika wurin babban sarki don neman taimako. Amma bai iya warkar da kai ba, bai iya warkar da miyakunka ba.
14 For I will be unto Ephraim as a lion, and as a young lion to the house of Judah; I, even I, will tear and go away, I will take away, and there shall be none to deliver.
Gama zan zama kamar zaki ga Efraim, kamar babban zaki ga Yahuda. Zan yage su kucu-kucu in tafi; zan kwashe su, ba wanda zai kuɓutar da su.
15 I will go and return to My place, till they acknowledge their guilt, and seek My face; in their trouble they will seek Me earnestly:
Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”