< Hosea 12 >
1 Ephraim striveth after wind, and followeth after the east wind; all the day he multiplieth lies and desolation; and they make a covenant with Assyria, and oil is carried into Egypt.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 The LORD hath also a controversy with Judah, and will punish Jacob according to his ways, according to his doings will He recompense him.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 In the womb he took his brother by the heel, and by his strength he strove with a godlike being;
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 So he strove with an angel, and prevailed; he wept, and made supplication unto him; at Beth-el he would find him, and there he would speak with us;
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 But the LORD, the God of hosts, the LORD is His name.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Therefore turn thou to thy God; keep mercy and justice, and wait for thy God continually.
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 As for the trafficker, the balances of deceit are in his hand. He loveth to oppress.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 And Ephraim said: 'Surely I am become rich, I have found me wealth; in all my labours they shall find in me no iniquity that were sin.'
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 But I am the LORD thy God from the land of Egypt; I will yet again make thee to dwell in tents, as in the days of the appointed season.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 I have also spoken unto the prophets, and I have multiplied visions; and by the ministry of the prophets have I used similitudes.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 If Gilead be given to iniquity becoming altogether vanity, in Gilgal they sacrifice unto bullocks; yea, their altars shall be as heaps in the furrows of the field.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 And Jacob fled into the field of Aram, and Israel served for a wife, and for a wife he kept sheep.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 And by a prophet the LORD brought Israel up out of Egypt, and by a prophet was he kept.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Ephraim hath provoked most bitterly; therefore shall his blood be cast upon him, and his reproach shall his Lord return unto him.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.