< Ezekiel 22 >
1 Moreover the word of the LORD came unto me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 'Now, thou, son of man, wilt thou judge, wilt thou judge the bloody city? then cause her to know all her abominations.
“Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
3 And thou shalt say: Thus saith the Lord GOD: O city that sheddest blood in the midst of thee, that thy time may come, and that makest idols unto thyself to defile thee;
ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
4 thou art become guilty in thy blood that thou hast shed, and art defiled in thine idols which thou hast made; and thou hast caused thy days to draw near, and art come even unto thy years; therefore have I made thee a reproach unto the nations, and a mocking to all the countries!
kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
5 Those that are near, and those that are far from thee, shall mock thee, thou defiled of name and full of tumult.
Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
6 Behold, the princes of Israel, every one according to his might, have been in thee to shed blood.
“‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
7 In thee have they made light of father and mother; in the midst of thee have they dealt by oppression with the stranger; in thee have they wronged the fatherless and the widow.
A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
8 Thou hast despised My holy things, and hast profaned My sabbaths.
Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
9 In thee have been talebearers to shed blood; and in thee they have eaten upon the mountains; in the midst of thee they have committed lewdness.
A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
10 In thee have they uncovered their fathers' nakedness; in thee have they humbled her that was unclean in her impurity.
A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
11 And each hath committed abomination with his neighbour's wife; and each hath lewdly defiled his daughter-in-law; and each in thee hath humbled his sister, his father's daughter.
A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
12 In thee have they taken gifts to shed blood; thou hast taken interest and increase, and thou hast greedily gained of thy neighbours by oppression, and hast forgotten Me, saith the Lord GOD.
A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
13 Behold, therefore, I have smitten My hand at thy dishonest gain which thou hast made, and at thy blood which hath been in the midst of thee.
“‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
14 Can thy heart endure, or can thy hands be strong, in the days that I shall deal with thee? I the LORD have spoken it, and will do it.
Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
15 And I will scatter thee among the nations, and disperse thee through the countries; and I will consume thy filthiness out of thee.
Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
16 And thou shalt be profaned in thyself, in the sight of the nations; and thou shalt know that I am the LORD.'
Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
17 And the word of the LORD came unto me, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 'Son of man, the house of Israel is become dross unto Me; all of them are brass and tin and iron and lead, in the midst of the furnace; they are the dross of silver.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
19 Therefore thus saith the Lord GOD: Because ye are all become dross, therefore, behold, I will gather you into the midst of Jerusalem.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
20 As they gather silver and brass and iron and lead and tin into the midst of the furnace, to blow the fire upon it, to melt it; so will I gather you in Mine anger and in My fury, and I will cast you in, and melt you.
Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
21 Yea, I will gather you, and blow upon you with the fire of My wrath, and ye shall be melted in the midst thereof.
Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
22 As silver is melted in the midst of the furnace, so shall ye be melted in the midst thereof; and ye shall know that I the LORD have poured out My fury upon you.'
Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
23 And the word of the LORD came unto me, saying:
Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
24 'Son of man, say unto her: Thou art a land that is not cleansed, nor rained upon in the day of indignation.
“Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
25 There is a conspiracy of her prophets in the midst thereof, like a roaring lion ravening the prey; they have devoured souls, they take treasure and precious things, they have made her widows many in the midst thereof.
Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
26 Her priests have done violence to My law, and have profaned My holy things; they have put no difference between the holy and the common, neither have they taught difference between the unclean and the clean, and have hid their eyes from My sabbaths, and I am profaned among them.
Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
27 Her princes in the midst thereof are like wolves ravening the prey: to shed blood, and to destroy souls, so as to get dishonest gain.
Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
28 And her prophets have daubed for them with whited plaster, seeing falsehood, and divining lies unto them, saying: Thus saith the Lord GOD, when the LORD hath not spoken.
Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
29 The people of the land have used oppression, and exercised robbery, and have wronged the poor and needy, and have oppressed the stranger unlawfully.
Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
30 And I sought for a man among them, that should make up the hedge, and stand in the breach before Me for the land, that I should not destroy it; but I found none.
“Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
31 Therefore have I poured out Mine indignation upon them; I have consumed them with the fire of My wrath; their own way have I brought upon their heads, saith the Lord GOD.'
Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”