< Ezekiel 15 >

1 And the word of the LORD came unto me, saying:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 'Son of man, what is the vine-tree more than any tree, the vine branch which grew up among the trees of the forest?
“Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
3 Shall wood be taken thereof to make any work? or will men take a pin of it to hang any vessel thereon?
An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
4 Behold, it is cast into the fire for fuel; the fire hath devoured both the ends of it, and the midst of it is singed; is it profitable for any work?
Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
5 Behold, when it was whole, it was meet for no work; how much less, when the fire hath devoured it, and it is singed, shall it yet be meet for any work?
In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
6 Therefore thus saith the Lord GOD: As the vine-tree among the trees of the forest, which I have given to the fire for fuel, so do I give the inhabitants of Jerusalem.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
7 And I will set My face against them; out of the fire are they come forth, and the fire shall devour them; and ye shall know that I am the LORD, when I set My face against them.
Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
8 And I will make the land desolate, because they have acted treacherously, saith the Lord GOD.'
Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 15 >