< Exodus 5 >

1 And afterward Moses and Aaron came, and said unto Pharaoh: 'Thus saith the LORD, the God of Israel: Let My people go, that they may hold a feast unto Me in the wilderness.'
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 And Pharaoh said: 'Who is the LORD, that I should hearken unto His voice to let Israel go? I know not the LORD, and moreover I will not let Israel go.'
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 And they said: 'The God of the Hebrews hath met with us. Let us go, we pray thee, three days' journey into the wilderness, and sacrifice unto the LORD our God; lest He fall upon us with pestilence, or with the sword.'
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 And the king of Egypt said unto them: 'Wherefore do ye, Moses and Aaron, cause the people to break loose from their work? get you unto your burdens.'
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 And Pharaoh said: 'Behold, the people of the land are now many, and will ye make them rest from their burdens?'
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 And the same day Pharaoh commanded the taskmasters of the people, and their officers, saying:
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 'Ye shall no more give the people straw to make brick, as heretofore. Let them go and gather straw for themselves.
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 And the tale of the bricks, which they did make heretofore, ye shall lay upon them; ye shall not diminish aught thereof; for they are idle; therefore they cry, saying: Let us go and sacrifice to our God.
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 Let heavier work be laid upon the men, that they may labour therein; and let them not regard lying words.'
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 And the taskmasters of the people went out, and their officers, and they spoke to the people, saying: 'Thus saith Pharaoh: I will not give you straw.
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 Go yourselves, get you straw where ye can find it; for nought of your work shall be diminished.'
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 So the people were scattered abroad throughout all the land of Egypt to gather stubble for straw.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 And the taskmasters were urgent, saying: 'Fulfil your work, your daily task, as when there was straw.'
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 And the officers of the children of Israel, whom Pharaoh's taskmasters had set over them, were beaten, saying: 'Wherefore have ye not fulfilled your appointed task in making brick both yesterday and today as heretofore?'
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 Then the officers of the children of Israel came and cried unto Pharaoh, saying: 'Wherefore dealest thou thus with thy servants?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 There is no straw given unto thy servants, and they say to us: Make brick; and, behold, thy servants are beaten, but the fault is in thine own people.'
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 But he said: 'Ye are idle, ye are idle; therefore ye say: Let us go and sacrifice to the LORD.
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 Go therefore now, and work; for there shall no straw be given you, yet shall ye deliver the tale of bricks.'
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 And the officers of the children of Israel did see that they were set on mischief, when they said: 'Ye shall not diminish aught from your bricks, your daily task.'
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 And they met Moses and Aaron, who stood in the way, as they came forth from Pharaoh;
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 and they said unto them: 'The LORD look upon you, and judge; because ye have made our savour to be abhorred in the eyes of Pharaoh, and in the eyes of his servants, to put a sword in their hand to slay us.'
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 And Moses returned unto the LORD, and said: 'Lord, wherefore hast Thou dealt ill with this people? why is it that Thou hast sent me?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 For since I came to Pharaoh to speak in Thy name, he hath dealt ill with this people; neither hast Thou delivered Thy people at all.'
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”

< Exodus 5 >