< Exodus 18 >
1 Now Jethro, the priest of Midian, Moses' father-in-law, heard of all that God had done for Moses, and for Israel His people, how that the LORD had brought Israel out of Egypt.
Ana nan sai Yetro firist na Midiyan, kuma surukin Musa, ya ji duk abin da Allah ya yi wa Musa da mutanensa Isra’ila, da kuma yadda Ubangiji ya fitar da Isra’ila daga Masar.
2 And Jethro, Moses' father-in-law, took Zipporah, Moses' wife, after he had sent her away,
Bayan da Musa ya tura matarsa Ziffora gida, sai surukinsa Yetro ya karɓe ta
3 and her two sons; of whom the name of the one was Gershom; for he said: 'I have been a stranger in a strange land';
da’ya’yanta biyu maza. Ana kira ɗaya Gershom, domin Musa ya ce, “Na zama baƙo a baƙuwar ƙasa”;
4 and the name of the other was Eliezer: 'for the God of my father was my help, and delivered me from the sword of Pharaoh.'
ɗayan kuma Eliyezer, domin ya ce, “Allah mahaifina ya taimake ni ya cece ni daga takobin Fir’auna.”
5 And Jethro, Moses' father-in-law, came with his sons and his wife unto Moses into the wilderness where he was encamped, at the mount of God;
Yetro surukin Musa tare da’ya’yan Musa da matarsa suka zo wurin Musa a hamada, inda suka kafa sansani kusa da dutsen Allah
6 and he said unto Moses: 'I thy father-in-law Jethro am coming unto thee, and thy wife, and her two sons with her.'
Yetro ya riga ya aika wa Musa cewa, “Ni surukinka Yetro, ina zuwa wurinka tare da matarka da’ya’yanka maza biyu.”
7 And Moses went out to meet his father-in-law, and bowed down and kissed him; and they asked each other of their welfare; and they came into the tent.
Sai Musa ya tafi yă taryi surukinsa, ya sunkuya ya yi masa sumba. Suka gai da juna, sa’an nan suka shiga tenti.
8 And Moses told his father-in-law all that the LORD had done unto Pharaoh and to the Egyptians for Israel's sake, all the travail that had come upon them by the way, and how the LORD delivered them.
Musa kuwa ya faɗa wa surukinsa duk abubuwan da Ubangiji ya yi wa Fir’auna da Masarawa domin Isra’ila, da batun wahalolin da suka sha a hanya, da yadda Ubangiji ya cece su.
9 And Jethro rejoiced for all the goodness which the LORD had done to Israel, in that He had delivered them out of the hand of the Egyptians.
Yetro ya yi murna da jin duk abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi wa Isra’ila, wajen cetonsu daga hannun Masarawa.
10 And Jethro said: 'Blessed be the LORD, who hath delivered you out of the hand of the Egyptians, and out of the hand of Pharaoh; who hath delivered the people from under the hand of the Egyptians.
“Yabo ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da na Fir’auna, wanda kuma ya cece mutanensa daga hannun Masarawa.
11 Now I know that the LORD is greater than all gods; yea, for that they dealt proudly against them.'
Yanzu na san cewa Ubangiji ya fi kowane allah, gama ya yi wannan ga masu girman kai da kuma waɗanda suka wulaƙanta Isra’ila.”
12 And Jethro, Moses' father-in-law, took a burnt-offering and sacrifices for God; and Aaron came, and all the elders of Israel, to eat bread with Moses' father-in-law before God.
Sa’an nan Yetro surukin Musa, ya kawo hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu wa Allah, Haruna ya zo tare da dukan dattawan Isra’ila, suka ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah.
13 And it came to pass on the morrow, that Moses sat to judge the people; and the people stood about Moses from the morning unto the evening.
Kashegari, Musa ya zauna domin yă yi wa mutane shari’a, sai suka tsaya kewaye da shi daga safe har yamma.
14 And when Moses' father-in-law saw all that he did to the people, he said: 'What is this thing that thou doest to the people? why sittest thou thyself alone, and all the people stand about thee from morning unto even?'
Sa’ad da surukinsa ya lura da duk abin da Musa yake yi saboda mutane, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa mutane? Don me kai kaɗai kake zama kana yin shari’a wa mutane, yayinda mutanen nan suke tsaya kewaye da kai daga safe har yamma?”
15 And Moses said unto his father-in-law: 'Because the people come unto me to inquire of God;
Musa ya amsa ya ce, “Saboda mutanen suna zuwa wurina, don su nemi nufin Allah.
16 when they have a matter, it cometh unto me; and I judge between a man and his neighbour, and I make them know the statutes of God, and His laws.'
Duk lokacin da suke da gardama, akan kawo su a wurina, ni kuma sai in raba tsakaninsu, in kuma koya musu dokokin Allah da farillansa.”
17 And Moses' father-in-law said unto him: 'The thing that thou doest is not good.
Surukin Musa ya amsa ya ce, “Abin da kake yi ba daidai ba ne.
18 Thou wilt surely wear away, both thou, and this people that is with thee; for the thing is too heavy for thee; thou art not able to perform it thyself alone.
Kai da dukan mutanen da suke zuwa wurinka za ku gajiyar da kanku. Aikin ya fi ƙarfinka; ba za ka iya yinsa kai kaɗai ba.
19 Hearken now unto my voice, I will give thee counsel, and God be with thee: be thou for the people before God, and bring thou the causes unto God.
Ka kasa kunne gare ni yanzu, zan ba ka shawara, Allah kuma yă kasance tare da kai. Kai za ka zama wakilin mutane a gaban Allah, ka kuma kawo gardamansu gare shi.
20 And thou shalt teach them the statutes and the laws, and shalt show them the way wherein they must walk, and the work that they must do.
Ka koya musu dokokinsa da farillarsa, ka kuma nuna musu hanyar rayuwa da ayyukan da za su yi.
21 Moreover thou shalt provide out of all the people able men, such as fear God, men of truth, hating unjust gain; and place such over them, to be rulers of thousands, rulers of hundreds, rulers of fifties, and rulers of tens.
Amma ka zaɓi mutane masu iyawa daga dukan mutane, maza masu tsoron Allah, amintattu, masu ƙin rashawa, ka sanya su shugabanni na dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
22 And let them judge the people at all seasons; and it shall be, that every great matter they shall bring unto thee, but every small matter they shall judge themselves; so shall they make it easier for thee and bear the burden with thee.
Bari waɗannan mutane su sassanta mutane a kan ƙananan matsaloli, amma kowace babban matsala, ko bukata ta musamman, sai su kawo wurinka, ƙananan matsaloli kuma sai su yanke hukuncin da kansu. Ta haka ne za su taimaka wajen ɗaukan nauyin jama’a, don su sa aikin yă zama maka da sauƙi.
23 If thou shalt do this thing, and God command thee so, then thou shalt be able to endure, and all this people also shall go to their place in peace.'
In ka yi haka, Allah ya umarta za ka iya jimre gajiyar, kuma dukan mutanen nan za su koma gida da murna.”
24 So Moses hearkened to the voice of his father-in-law, and did all that he had said.
Musa ya kasa kunne ga surukinsa, ya kuma aikata duk abin da ya faɗa.
25 And Moses chose able men out of all Israel, and made them heads over the people, rulers of thousands, rulers of hundreds, rulers of fifties, and rulers of tens.
Ya zaɓi mutane masu iyawa daga cikin dukan Isra’ila, ya naɗa su shugabannin mutane, shugabanni a kan dubbai, ɗari-ɗari, hamsin-hamsin da goma-goma.
26 And they judged the people at all seasons: the hard causes they brought unto Moses, but every small matter they judged themselves.
Suka yi hidimar alƙalanci na mutane a dukan lokaci. Gardandamin da suke da wuya, suka kawo wurin Musa, amma ƙananan batuttuwa, suka shari’anta a tsakaninsu.
27 And Moses let his father-in-law depart; and he went his way into his own land.
Sa’an nan Musa ya sallame surukinsa Yetro, ya kuwa koma ƙasarsa.