< 2 Kings 20 >

1 In those days was Hezekiah sick unto death. And Isaiah the prophet the son of Amoz came to him, and said unto him: 'Thus saith the LORD: Set thy house in order; for thou shalt die, and not live.'
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
2 Then he turned his face to the wall, and prayed unto the LORD, saying:
Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
3 'Remember now, O LORD, I beseech Thee, how I have walked before Thee in truth and with a whole heart, and have done that which is good in Thy sight.' And Hezekiah wept sore.
“Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 And it came to pass, before Isaiah was gone out of the inner court of the city, that the word of the LORD came to him, saying:
Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
5 'Return, and say to Hezekiah the prince of My people: Thus saith the LORD, the God of David thy father: I have heard thy prayer, I have seen thy tears; behold, I will heal thee; on the third day thou shalt go up unto the house of the LORD.
“Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
6 And I will add unto thy days fifteen years; and I will deliver thee and this city out of the hand of the king of Assyria; and I will defend this city for Mine own sake, and for My servant David's sake.'
Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
7 And Isaiah said: 'Take a cake of figs.' And they took and laid it on the boil, and he recovered.
Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
8 And Hezekiah said unto Isaiah: 'What shall be the sign that the LORD will heal me, and that I shall go up unto the house of the LORD the third day?'
Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
9 And Isaiah said: 'This shall be the sign unto thee from the LORD, that the LORD will do the thing that He hath spoken: shall the shadow go forward ten degrees, or go back ten degrees?
Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
10 And Hezekiah answered: 'It is a light thing for the shadow to decline ten degrees; nay, but let the shadow return backward ten degrees.'
“Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
11 And Isaiah the prophet cried unto the LORD; and he brought the shadow ten degrees backward, by which it had gone down on the dial of Ahaz.
Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
12 At that time Berodach-baladan the son of Baladan, king of Babylon, sent a letter and a present unto Hezekiah; for he had heard that Hezekiah had been sick.
A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
13 And Hezekiah hearkened unto them, and showed them all his treasure-house, the silver, and the gold, and the spices, and the precious oil, and the house of his armour, and all that was found in his treasures; there was nothing in his house, nor in all his dominion, that Hezekiah showed them not.
Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
14 Then came Isaiah the prophet unto king Hezekiah, and said unto him: 'What said these men? and from whence came they unto thee?' And Hezekiah said: 'They are come from a far country, even from Babylon.'
Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
15 And he said: 'What have they seen in thy house?' And Hezekiah answered: 'All that is in my house have they seen; there is nothing among my treasures that I have not shown them.'
Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
16 And Isaiah said unto Hezekiah: 'Hear the word of the LORD.
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
17 Behold, the days come, that all that is in thy house, and that which thy fathers have laid up in store unto this day, shall be carried to Babylon; nothing shall be left, saith the LORD.
Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
18 And of thy sons that shall issue from thee, whom thou shalt beget, shall they take away; and they shall be officers in the palace of the king of Babylon.'
Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
19 Then said Hezekiah unto Isaiah: 'Good is the word of the LORD which thou hast spoken.' He said moreover: 'Is it not so, if peace and truth shall be in my days?'
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
20 Now the rest of the acts of Hezekiah, and all his might, and how he made the pool, and the conduit, and brought water into the city, are they not written in the book of the chronicles of the kings of Judah?
Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
21 And Hezekiah slept with his fathers; and Manasseh his son reigned in his stead.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Kings 20 >