< 2 Chronicles 6 >
1 Then spoke Solomon: The LORD hath said that He would dwell in the thick darkness.
Sa’an nan Solomon ya ce, “Ubangiji ya faɗa cewa zai zauna cikin duhun girgije;
2 But I have built Thee a house of habitation, and a place for Thee to dwell in for ever.
na gina ƙasaitaccen haikali dominka, wuri domin ka zauna har abada.”
3 And the king turned his face, and blessed all the congregation of Israel; and all the congregation of Israel stood.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
4 And he said: 'Blessed be the LORD, the God of Israel, who spoke with His mouth unto David my father, and hath with His hands fulfilled it, saying:
Sa’an nan ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannuwansa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
5 Since the day that I brought forth My people out of the land of Egypt, I chose no city out of all the tribes of Israel to build a house in, that My name might be there; neither chose I any man to be prince over My people Israel;
‘Tun ranar na da fitar da mutanena daga Masar, ban zaɓi wani birni a wata kabilar Isra’ila don a gina haikali domin Sunana ya kasance a can ba, ba kuwa zaɓi wani yă zama shugaba a bisa jama’ata Isra’ila ba.
6 but I have chosen Jerusalem, that My name might be there; and have chosen David to be over My people Israel.
Amma yanzu na zaɓi Urushalima domin Sunana yă kasance a can, na kuma zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
7 Now it was in the heart of David my father to build a house for the name of the LORD, the God of Israel.
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a zuciyarsa yă gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
8 But the LORD said unto David my father: Whereas it was in thy heart to build a house for My name, thou didst well that it was in thy heart;
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Domin yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka kasance da wannan a zuciyarka.
9 nevertheless thou shalt not build the house, but thy son that shall come forth out of thy loins, he shall build the house for My name.
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikalin, amma ɗanka wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
10 And the LORD hath established His word that He spoke; for I am risen up in the room of David my father, and sit on the throne of Israel, as the LORD promised, and have built the house for the name of the LORD, the God of Israel.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina yanzu kuwa na zauna a kan kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
11 And there have I set the ark, wherein is the covenant of the LORD, which He made with the children of Israel.'
A can na ajiye akwatin alkawari, inda alkawarin Ubangiji da ya yi da mutanen Isra’ila yake.”
12 And he stood before the altar of the LORD in the presence of all the congregation of Israel, and spread forth his hands —
Sa’an nan Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa sama.
13 for Solomon had made a brazen scaffold, of five cubits long, and five cubits broad, and three cubits high, and had set it in the midst of the court; and upon it he stood, and kneeled down upon his knees before all the congregation of Israel, and spread forth his hands toward heaven —
Dā ma ya riga ya gina dakalin tagulla, mai tsawo kamu biyar, fāɗi kamu biyar da kuma tsayi kamu uku, ya kuma sa shi a tsakiyar filin waje. Ya tsaya a kan dakalin ya kuma durƙusa a gaban dukan taron Isra’ila ya buɗe hannuwansa sama.
14 and he said: 'O LORD, the God of Israel, there is no God like Thee, in the heaven, or in the earth; who keepest covenant and mercy with Thy servants, that walk before Thee with all their heart;
Ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama da kuma ƙasa, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna tare da bayinka waɗanda suke cin gaba da zuciya ɗaya a hanyarka.
15 who hast kept with Thy servant David my father that which Thou didst promise him; yea, Thou spokest with Thy mouth, and hast fulfilled it with Thy hand, as it is this day.
Ka kiyaye alkawarinka ga bawanka Dawuda mahaifina; da bakinka ka yi alkawari kuma da hannunka ka cika shi, yadda yake a yau.
16 Now therefore, O LORD, the God of Israel, keep with Thy servant David my father that which Thou hast promised him, saying: There shall not fail thee a man in My sight to sit on the throne of Israel; if only thy children take heed to their way, to walk in My law as thou hast walked before Me.
“Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka kiyaye wa bawanka Dawuda mahaifina alkawuran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka kāsa kasance da mutumin da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza za su kula cikin dukan abin da suke yi su yi tafiya a gabana bisa ga dokata, kamar yadda ka yi.’
17 Now therefore, O LORD, the God of Israel, let Thy word be verified, which Thou spokest unto Thy servant David.
Yanzu kuwa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi alkawarta wa bawanka Dawuda yă cika.
18 But will God in very truth dwell with men on the earth? behold, heaven and the heaven of heavens cannot contain Thee; how much less this house which I have builded!
“Amma tabbatacce Allah zai zauna a duniya tare da mutane? Sammai, har ma da saman sammai, ba za su iya riƙe ka ba. Balle wannan haikalin da na gina!
19 Yet have Thou respect unto the prayer of Thy servant, and to his supplication, O LORD my God, to hearken unto the cry and to the prayer which Thy servant prayeth before Thee;
Duk da haka ka mai da hankali ga addu’ar bawanka da kuma roƙo don jinƙai, ya Ubangiji, Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.
20 that Thine eyes may be open toward this house day and night, even toward the place whereof Thou hast said that thou wouldest put Thy name there; to hearken unto the prayer which Thy servant shall pray toward this place.
Bari idanunka su buɗu ta wajen wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce za ka sa Sunanka a can. Bari ka ji addu’ar da bawanka ke yi ta wajen wannan wuri.
21 And hearken Thou to the supplications of Thy servant, and of Thy people Israel, when they shall pray toward this place; yea, hear Thou from Thy dwelling-place, even from heaven; and when Thou hearest, forgive.
Ka ji roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a suna duban wajen wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka; kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
22 If a man sin against his neighbour, and an oath be exacted of him to cause him to swear, and he come and swear before Thine altar in this house;
“Sa’ad da mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi aka kuma bukaci ya yi rantsuwa, ya kuma zo ya rantse a gaban bagadenka a cikin wannan haikali,
23 then hear Thou from heaven, and do, and judge Thy servants, requiting the wicked, to bring his way upon his own head; and justifying the righteous, to give him according to his righteousness.
sai ka ji daga sama ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, kana sāka wa mai laifi ta wurin kawo a kansa hakkin abin da ya yi. Ka nuna cewa marar laifi ba shi da laifi, ta haka a fiffita rashin laifinsa.
24 And if Thy people Israel be smitten down before the enemy, when they sin against Thee, and shall turn again and confess Thy name, and pray and make supplication before Thee in this house;
“Sa’ad da an ci mutanenka Isra’ila a yaƙi ta wurin abokin gāba domin sun yi maka zunubi kuma sa’ad da suka juya suka furta sunanka, suna addu’a suka kuma yin roƙe-roƙe a gabanka a wannan haikali,
25 then hear Thou from heaven, and forgive the sin of Thy people Israel, and bring them back unto the land which Thou gavest to them and to their fathers.
sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin mutanenka Isra’ila ka kuma dawo da su zuwa ƙasar da ka ba su da kuma kakanninsu.
26 When the heaven is shut up, and there is no rain, when they sin against Thee; if they pray toward this place, and confess Thy name, turning from their sin, when Thou dost afflict them;
“Sa’ad da sammai suka rufu ba kuwa ruwan sama saboda mutanenka sun yi maka zunubi, sa’ad da kuwa suka yi addu’a suna duban waje wannan wuri suka kuma furta sunanka suka juye daga zunubinsu domin ka azabta su,
27 then hear Thou in heaven, and forgive the sin of Thy servants, and of Thy people Israel, when Thou dost direct them on the good way wherein they should walk; and send rain upon Thy land, which Thou hast given to Thy people for an inheritance.
sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace da za su yi zama, ka kuma aika ruwan sama a ƙasar da ka ba mutanenka gādo.
28 If there be in the land famine, if there be pestilence, if there be blasting or mildew, locust or caterpillar; if their enemies besiege them in the land of their cities; whatsoever plague or whatsoever sickness there be;
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko wahala ko fumfuna, ko fāra ko fāra ɗango, ko sa’ad da abokan gāba sun yi musu ƙawanya a kowane daga biranensu, dukan wata masifa ko cutar da za tă zo,
29 what prayer and supplication soever be made by any man, or by all Thy people Israel, who shall know every man his own plague and his own pain, and shall spread forth his hands toward this house;
sa’ad da kuwa wani cikin mutanenka Isra’ila ya yi wata addu’a ko roƙo, kowa yana sane a azabarsa da kuma zafinsa, yana buɗe hannuwansa yana duban wajen wannan haikali,
30 then hear Thou from heaven Thy dwelling-place, and forgive, and render unto every man according to all his ways, whose heart Thou knowest — for Thou, even Thou only, knowest the hearts of the children of men —
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi da kowane mutum gwargwadon duk abin da yake yi, da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan mutane),
31 that they may fear Thee, to walk in Thy ways, all the days that they live in the land which Thou gavest unto our fathers.
don su ji tsoronka su kuma yi tafiya a hanyoyinka a kowane lokacin da suke zama a ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
32 Moreover concerning the stranger, that is not of Thy people Israel, when be shall come out of a far country for Thy great name's sake, and Thy mighty hand, and Thine outstretched arm; when they shall come and pray toward this house;
“Game da baƙo wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba kuwa amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka mai girma da kuma hannunka mai iko da hannunka mai ƙarfi, sa’ad da ya zo ya yi addu’a yana duban wannan haikali,
33 then hear Thou from heaven, even from Thy dwelling-place, and do according to all that the stranger calleth to Thee for; that all the peoples of the earth may know Thy name, and fear Thee, as doth Thy people Israel, and that they may know that Thy name is called upon this house which I have built.
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi duk abin da baƙon ya nemi ka yi, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, su kuma san cewa wannan gidan da na gina na Sunanka ne.
34 If Thy people go out to battle against their enemies, by whatsoever way Thou shalt send them, and they pray unto Thee toward this city which Thou hast chosen, and the house which I have built for Thy name;
“Sa’ad da mutanenka suka je yaƙi da abokan gābansu, ko’ina ka kai su, kuma sa’ad da suka yi addu’a gare ka suna duban wannan birnin da ka zaɓa da haikalin nan da na gina domin Sunanka,
35 then hear Thou from heaven their prayer and their supplication, and maintain their cause.
sai ka ji addu’arsu da kuma roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatarsu.
36 If they sin against Thee — for there is no man that sinneth not — and Thou be angry with them, and deliver them to the enemy, so that they carry them away captive unto a land far off or near;
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
37 yet if they shall bethink themselves in the land whither they are carried captive, and turn, and make supplication unto Thee in the land of their captivity, saying: We have sinned, we have done iniquitously, and have dealt wickedly;
Kuma in suka canja zuciya a cikin ƙasar da suke zaman bauta, suka tuba suka roƙe ka a ƙasar zaman bautarsu suka kuma ce, ‘Mun yi zunubi, mu yi abin da ba daidai ba, mu kuwa yi mugunta’;
38 if they return unto Thee with all their heart and with all their soul in the land of their captivity, whither they have carried them captive, and pray toward their land, which Thou gavest unto their fathers, and the city which Thou hast chosen, and toward the house which I have built for Thy name;
in kuma sun juye gare ka da dukan zuciyarsu da ransu a ƙasar zaman bautarsu inda aka kai su, suka kuma dubi wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, wajen birnin da ka zaɓa da kuma wajen haikalin da na gina domin Sunanka;
39 then hear Thou from heaven, even from Thy dwelling-place, their prayer and their supplications, and maintain their cause; and forgive Thy people who have sinned against Thee.
to, daga sama, mazauninka, sai ka ji addu’arsu da kuma roƙe-roƙensu, ka kuwa biya musu bukatunsu. Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi.
40 Now, O my God, let, I beseech Thee, Thine eyes be open, and let Thine ears be attent, unto the prayer that is made in this place.
“Yanzu, Allahna, bari idanunka su buɗu kunnuwanka kuma su saurara ga addu’o’in da ake miƙa a wannan wuri.
41 Now therefore arise, O LORD God, into Thy resting-place, Thou, and the ark of Thy strength; let Thy priests, O LORD God, be clothed with salvation, and let Thy saints rejoice in good.
“Yanzu ka tashi, ya Ubangiji Allah, ka zo wurin hutunka,
42 O LORD God, turn not away the face of Thine anointed; remember the good deeds of David Thy servant.'
Ya Ubangiji Allah, kada ka ƙyale shafaffenka.