< 2 Chronicles 28 >
1 Ahaz was twenty years old when he began to reign; and he reigned sixteen years in Jerusalem; and he did not that which was right in the eyes of the LORD, like David his father;
Ahaz yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Ba kamar Dawuda kakansa ba, bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ba.
2 but he walked in the ways of the kings of Israel, and made also molten images for the Baalim.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila ya kuma yi zubin gumaka domin a bauta wa Ba’al.
3 Moreover he offered in the valley of the son of Hinnom, and burnt his children in the fire, according to the abominations of the heathen, whom the LORD cast out before the children of Israel.
Ya ƙone hadayu a Kwarin Ben Hinnom, ya kuma miƙa’ya’yansa maza a cikin wuta, yana bin hanyoyi banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
4 And he sacrificed and offered in the high places, and on the hills, and under every leafy tree.
Ya miƙa hadayu, ya kuma ƙone turare a masujadan kan tudu, a bisa tuddai da kuma ƙarƙashin kowane itace mai inuwa.
5 Wherefore the LORD his God delivered him into the hand of the king of Aram; and they smote him, and carried away of his a great multitude of captives, and brought them to Damascus. And he was also delivered into the hand of the king of Israel, who smote him with a great slaughter.
Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya miƙa shi ga sarkin Aram. Arameyawa suka ci shi a yaƙi, suka kuma kwashe mutanensa da yawa a matsayin’yan kurkuku, suka kawo Damaskus. Ya kuma ba da shi ga sarkin Isra’ila, wanda ya jijji masa a yaƙi.
6 For Pekah the son of Remaliah slew in Judah a hundred and twenty thousand in one day, all of them valiant men; because they had forsaken the LORD, the God of their fathers.
A rana ɗaya Feka ɗan Remaliya ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu ashirin a Yahuda, domin Yahuda sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu.
7 And Zichri, a mighty man of Ephraim, slew Maaseiah the king's son, and Azrikam the ruler of the house, and Elkanah that was next to the king.
Zikri, wani jarumin Efraim, ya kashe Ma’asehiya ɗan sarki, Azrikam hafsa mai lura da fada, da kuma Elkana, mataimakin sarki.
8 And the children of Israel carried away captive of their brethren two hundred thousand women, sons, and daughters, and took also away much spoil from them, and brought the spoil to Samaria.
Isra’ilawa suka kame kamammu daga’yan’uwansu mata,’ya’ya maza da kuma’ya’ya mata dubu ɗari biyu. Suka kuma kwashe ganima mai yawan gaske, waɗanda suka kwasa zuwa Samariya.
9 But a prophet of the LORD was there, whose name was Oded; and he went out to meet the host that came to Samaria, and said unto them: 'Behold, because the LORD, the God of your fathers, was wroth with Judah, He hath delivered them into your hand, and ye have slain them in a rage which hath reached up unto heaven.
Amma wani annabin Ubangiji mai suna Oded yana a can, sai ya fito don yă sadu da mayaƙa sa’ad da suke komowa zuwa Samariya. Ya ce musu, “Domin Ubangiji Allah na kakanninku yana fushi da Yahuda, ya ba da su cikin hannunku. Sai kuka kashe su cikin fushin da ya kai sama.
10 And now ye purpose to bring the children of Judah and Jerusalem into subjection for bondmen and bondwomen unto you; but are there not even with you acts of guilt of your own against the LORD your God?
Yanzu kuma kuna niyya ku mai da maza da matan Yahuda da Urushalima bayinku. Amma ku ɗin ba ku da laifin zunubi ga Ubangiji Allahnku ne?
11 Now hear me therefore, and send back the captives, that ye have taken captive of your brethren; for the fierce wrath of the LORD is upon you.'
To, ku saurare ni! Ku mai da’yan’uwanku da kuka kama a matsayin’yan kurkuku, gama fushin Ubangiji yana a kanku.”
12 Then certain of the heads of the children of Ephraim, Azariah the son of Jehohanan, Berechiah the son of Meshillemoth, and Jehizkiah the son of Shallum, and Amasa the son of Hadlai, stood up against them that came from the war,
Sai waɗansu shugabanni a Efraim, Azariya ɗan Yehohanan, Berekiya ɗan Meshillemot, Hezekiya ɗan Shallum da Amasa ɗan Hadlai, suka tasar wa waɗanda suke isowa daga yaƙi.
13 and said unto them: 'Ye shall not bring in the captives hither; for ye purpose that which will bring upon us guilt against the LORD, to add unto our sins and to our guilt; for our guilt is great, and there is fierce wrath against Israel.'
Suka ce, “Dole ku kawo waɗannan’yan kurkukun a nan, ko kuwa za ku yi laifi a gaban Ubangiji. Kuna niyya ku ƙara ga zunubinmu da kuma laifinmu? Gama laifinmu ya riga ya yi yawa, kuma fushinsa mai tsanani yana a kan Isra’ila.”
14 So the armed men left the captives and the spoil before the princes and all the congregation.
Saboda haka sojoji suka ba da’yan kurkukun da ganima a gaban hafsoshi da dukan taron.
15 And the men that have been mentioned by name rose up, and took the captives, and with the spoil clothed all that were naked among them, and arrayed them, and shod them, and gave them to eat and to drink, and anointed them, and carried all the feeble of them upon asses, and brought them to Jericho, the city of palm-trees, unto their brethren; then they returned to Samaria.
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
16 At that time did king Ahaz send unto the kings of Assyria to help him.
A lokacin nan Sarki Ahaz ya aika wurin sarkin Assuriya neman taimako.
17 For again the Edomites had come and smitten Judah, and carried away captives.
Mutanen Edom sun sāke zuwa suka yaƙi Yahuda suka kuma kwashe’yan kurkuku,
18 The Philistines also had invaded the cities of the Lowland, and of the South of Judah, and had taken Beth-shemesh, and Aijalon, and Gederoth, and Soco with the towns thereof, and Timnah with the towns thereof, Gimzo also and the towns thereof; and they dwelt there.
yayinda Filistiyawa suka kai hari wa garuruwa a gindin tuddai da kuma a Negeb na Yahuda. Suka kame su suka kuma zauna a Bet-Shemesh, Aiyalon da Gederot, haka ma Soko, Timna da Gimzo tare da ƙauyuka kewayensu.
19 For the LORD brought Judah low because of Ahaz king of Israel; for he had cast away restraint in Judah, and acted treacherously against the LORD.
Ubangiji ya ƙasƙantar da Yahuda saboda Ahaz sarkin Isra’ila, gama ya hadasa mugunta a Yahuda kuma ya kasance marar aminci ga Ubangiji.
20 And Tillegath-pilneser king of Assyria came unto him, and distressed him, but strengthened him not.
Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo wurinsa, sai ya wahalar da sarki Ahaz maimakon taimakonsa.
21 For Ahaz stripped the house of the LORD, and the house of the king and the princes, and gave thereof unto the king of Assyria; but it helped him not.
Ahaz ya ɗauki waɗansu abubuwa daga haikalin Ubangiji da kuma daga fadan sarki da kuma daga sarakuna, ya ba da su ga sarkin Assuriya, amma wannan bai taimake shi ba.
22 And in the time of his distress did he act even more treacherously against the LORD, this same king Ahaz.
Cikin lokacin wahalarsa Sarki Ahaz ya ƙara zama marar aminci ga Ubangiji.
23 For he sacrificed unto the gods of Damascus, which smote him; and he said: 'Because the gods of the kings of Aram helped them, therefore will I sacrifice to them, that they may help me.' But they were the ruin of him, and of all Israel.
Ya miƙa hadayu ga allolin Damaskus, waɗanda suka ci shi a yaƙi; gama ya yi tunani, “Da yake allolin sarakunan Aram sun taimake su, zan miƙa hadayu domin su taimake ni.” Amma suka zama sanadin fāɗuwarsa da kuma fāɗuwar dukan Isra’ila.
24 And Ahaz gathered together the vessels of the house of God, and cut in pieces the vessels of the house of God, and shut up the doors of the house of the LORD; and he made him altars in every corner of Jerusalem.
Ahaz ya tattara kayayyaki daga haikalin Allah ya kwashe su. Ya kulle ƙofofin haikalin Ubangiji ya kakkafa bagadai a kowace kusurwa a titin Urushalima.
25 And in every city of Judah he made high places to offer unto other gods, and provoked the LORD, the God of his fathers.
A kowane gari a Yahuda, ya gina masujadan kan tudu don ƙone hadayu ga waɗansu alloli, ya kuma tsokane Ubangiji Allah na kakanninsa ya yi fushi.
26 Now the rest of his acts, and all his ways, first and last, behold, they are written in the book of the kings of Judah and Israel.
Sauran ayyukan mulkinsa da dukan hanyoyinsa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 And Ahaz slept with his fathers, and they buried him in the city, even in Jerusalem; for they brought him not into the sepulchres of the kings of Israel; and Hezekiah his son reigned in his stead.
Ahaz ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Urushalima, amma ba a sa shi a makabartan sarakunan Isra’ila ba. Sai Hezekiya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.