< 1 Samuel 29 >

1 Now the Philistines gathered together all their hosts to Aphek; and the Israelites pitched by the fountain which is in Jezreel.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 And the lords of the Philistines passed on by hundreds, and by thousands; and David and his men passed on in the rearward with Achish.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 Then said the princes of the Philistines: 'What do these Hebrews here?' And Achish said unto the princes of the Philistines: 'Is not this David, the servant of Saul the king of Israel, who hath been with me these days or these years, and I have found no fault in him since he fell away unto me unto this day?'
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 But the princes of the Philistines were wroth with him; and the princes of the Philistines said unto him: 'Make the man return, that he may go back to his place where thou hast appointed him, and let him not go down with us to battle, lest in the battle he become an adversary to us; for wherewith should this fellow reconcile himself unto his lord? should it not be with the heads of these men?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 Is not this David, of whom they sang one to another in dances, saying: Saul hath slain his thousands, and David his ten thousands?'
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 Then Achish called David, and said unto him: 'As the LORD liveth, thou hast been upright, and thy going out and thy coming in with me in the host is good in my sight; for I have not found evil in thee since the day of thy coming unto me unto this day; nevertheless the lords favour thee not.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Wherefore now return, and go in peace, that thou displease not the lords of the Philistines.'
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 And David said unto Achish: 'But what have I done? and what hast thou found in thy servant so long as I have been before thee unto this day, that I may not go and fight against the enemies of my lord the king?'
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 And Achish answered and said to David: 'I know that thou art good in my sight, as an angel of God; notwithstanding the princes of the Philistines have said: He shall not go up with us to the battle.
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 Wherefore now rise up early in the morning with the servants of thy lord that are come with thee; and as soon as ye are up early in the morning, and have light, depart.'
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 So David rose up early, he and his men, to depart in the morning, to return into the land of the Philistines. And the Philistines went up to Jezreel.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.

< 1 Samuel 29 >