< 1 Kings 5 >
1 And Hiram king of Tyre sent his servants unto Solomon; for he had heard that they had anointed him king in the room of his father; for Hiram was ever a lover of David.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 And Solomon sent to Hiram, saying:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 'Thou knowest how that David my father could not build a house for the name of the LORD his God for the wars which were about him on every side, until the LORD put them under the soles of my feet.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 But now the LORD my God hath given me rest on every side; there is neither adversary, nor evil occurrence.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 And, behold, I purpose to build a house for the name of the LORD my God, as the LORD spoke unto David my father, saying: Thy son, whom I will set upon thy throne in thy room, he shall build the house for My name.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 Now therefore command thou that they hew me cedar-trees out of Lebanon; and my servants shall be with thy servants; and I will give thee hire for thy servants according to all that thou shalt say; for thou knowest that there is not among us any that hath skill to hew timber like unto the Zidonians.'
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 And it came to pass, when Hiram heard the words of Solomon, that he rejoiced greatly, and said: 'Blessed be the LORD this day, who hath given unto David a wise son over this great people.'
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 And Hiram sent to Solomon, saying: 'I have heard that which thou hast sent unto me; I will do all thy desire concerning timber of cedar, and concerning timber of cypress.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 My servants shall bring them down from Lebanon unto the sea; and I will make them into rafts to go by sea unto the place that thou shalt appoint me, and will cause them to be broken up there, and thou shalt receive them; and thou shalt accomplish my desire, in giving food for my household.'
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 So Hiram gave Solomon timber of cedar and timber of cypress according to all his desire.
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 And Solomon gave Hiram twenty thousand measures of wheat for food to his household, and twenty measures of beaten oil; thus gave Solomon to Hiram year by year.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 And the LORD gave Solomon wisdom, as He promised him; and there was peace between Hiram and Solomon; and they two made a league together.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 And king Solomon raised a levy out of all Israel; and the levy was thirty thousand men.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 And he sent them to Lebanon, ten thousand a month by courses: a month they were in Lebanon, and two months at home; and Adoniram was over the levy.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 And Solomon had threescore and ten thousand that bore burdens, and fourscore thousand that were hewers in the mountains;
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 besides Solomon's chief officers that were over the work, three thousand and three hundred, who bore rule over the people that wrought in the work.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 And the king commanded, and they quarried great stones, costly stones, to lay the foundation of the house with hewn stone.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 And Solomon's builders and Hiram's builders and the Gebalites did fashion them, and prepared the timber and the stones to build the house.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.