< 1 Chronicles 15 >

1 And David made him houses in the city of David; and he prepared a place for the ark of God, and pitched for it a tent.
Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
2 Then David said: 'None ought to carry the ark of God but the Levites; for them hath the LORD chosen to carry the ark of the LORD, and to minister unto Him for ever.'
Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
3 And David assembled all Israel at Jerusalem, to bring up the ark of the LORD unto its place, which he had prepared for it.
Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
4 And David gathered together the sons of Aaron, and the Levites;
Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
5 of the sons of Kohath: Uriel the chief, and his brethren a hundred and twenty;
Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
6 of the sons of Merari: Asaiah the chief, and his brethren two hundred and twenty;
daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
7 of the sons of Gershom: Joel the chief, and his brethren a hundred and thirty;
daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
8 of the sons of Elizaphan: Shemaiah the chief, and his brethren two hundred;
daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
9 of the sons of Hebron: Eliel the chief, and his brethren fourscore;
daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
10 of the sons of Uzziel: Amminadab the chief, and his brethren a hundred and twelve.
daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
11 And David called for Zadok and Abiathar the priests, and for the Levites, for Uriel, Asaiah, and Joel, Shemaiah, and Eliel, and Amminadab,
Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
12 and said unto them: 'Ye are the heads of the fathers' houses of the Levites; sanctify yourselves, both ye and your brethren, that ye may bring up the ark of the LORD, the God of Israel, unto the place that I have prepared for it.
Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
13 For because ye bore it not at the first, the LORD our God made a breach upon us, for that we sought Him not according to the ordinance.'
Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
14 So the priests and the Levites sanctified themselves to bring up the ark of the LORD, the God of Israel.
Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
15 And the children of the Levites bore the ark of God upon their shoulders with the bars thereon, as Moses commanded according to the word of the LORD.
Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
16 And David spoke to the chief of the Levites to appoint their brethren the singers, with instruments of music, psalteries and harps and cymbals, sounding aloud and lifting up the voice with joy.
Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
17 So the Levites appointed Heman the son of Joel; and of his brethren, Asaph the son of Berechiah; and of the sons of Merari their brethren, Ethan the son of Kushaiah;
Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
18 and with them their brethren of the second degree, Zechariah, Ben, and Jaaziel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Unni, Eliab, and Benaiah, and Maaseiah, and Mattithiah, and Eliphalehu, and Mikneiah, and Obed-edom, and Jeiel, the doorkeepers.
Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
19 So the singers, Heman, Asaph, and Ethan, were appointed, with cymbals of brass to sound aloud;
Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
20 and Zechariah, and Aziel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Unni, and Eliab, and Maaseiah, and Benaiah, with psalteries set to Alamoth;
Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
21 and Mattithiah, and Eliphalehu, and Mikneiahu, and Obed-edom, and Jeiel, and Azaziah, with harps on the Sheminith, to lead.
Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
22 And Chenaniah, chief of the Levites, was over the song; he was master in the song, because he was skilful.
Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
23 And Berechiah and Elkanah were door-keepers for the ark.
Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
24 And Shebaniah, and Joshaphat, and Nethanel, and Amasai, and Zechariah, and Benaiah, and Eliezer, the priests, did blow with the trumpets before the ark of God; and Obed-edom and Jehiah were doorkeepers for the ark.
Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
25 So David, and the elders of Israel, and the captains over thousands, went to bring up the ark of the covenant of the LORD out of the house of Obed-edom with joy.
Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
26 And it came to pass, when God helped the Levites that bore the ark of the covenant of the LORD, that they sacrificed seven bullocks and seven rams.
Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
27 And David was clothed with a robe of fine linen, and all the Levites that bore the ark, and the singers, and Chenaniah the master of the singers in the song; and David had upon him an ephod of linen.
To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
28 Thus all Israel brought up the ark of the covenant of the LORD with shouting, and with sound of the horn, and with trumpets, and with cymbals, sounding aloud with psalteries and harps.
Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
29 And it came to pass, as the ark of the covenant of the LORD came to the city of David, that Michal the daughter of Saul looked out at the window, and saw king David dancing and making merry; and she despised him in her heart.
Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.

< 1 Chronicles 15 >