< 1 Chronicles 13 >

1 And David consulted with the captains of thousands and of hundreds, even with every leader.
Sai Dawuda ya tattauna da kowane ɗaya daga cikin shugabanninsa, shugabannin sojoji na dubu-dubu da na ɗari-ɗari.
2 And David said unto all the assembly of Israel: 'If it seem good unto you, and if it be of the LORD our God, let us send abroad everywhere unto our brethren that are left in all the land of Israel, and with them to the priests and Levites that are in their cities that have open land about them, that they may gather themselves unto us;
Sa’an nan ya ce wa dukan taron Isra’ila, “In ya yi muku kyau kuma in nufin Ubangiji Allahnmu ne, bari mu aika da saƙo nesa da kuma ko’ina zuwa ga sauran’yan’uwanmu a duk iyakokin Isra’ila, da kuma zuwa ga firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a garuruwansu da makiyayansu, su zo wurinmu.
3 and let us bring back the ark of our God to us; for we sought not unto it in the days of Saul.'
Bari mu ɗauko akwatin alkawarin Allahnmu mu kawo wurinmu, gama ba mu neme shi a lokacin mulkin Shawulu ba.”
4 And all the assembly said that they would do so; for the thing was right in the eyes of all the people.
Dukan taron jama’a suka yarda su yi haka, domin ya yi daidai ga dukan mutane.
5 So David assembled all Israel together, from Shihor the brook of Egypt even unto the entrance of Hamath, to bring the ark of God from Kiriath-jearim.
Saboda haka Dawuda ya tattara dukan Isra’ilawa, daga Kogin Shihor a Masar zuwa Lebo Hamat, don su kawo akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim.
6 And David went up, and all Israel, to Baalah, that is, to Kiriath-jearim, which belonged to Judah, to bring up from thence the ark of God, the LORD that sitteth upon the cherubim, whereon is called the Name.
Dawuda da dukan Isra’ilawa tare da shi suka tafi Ba’ala na Yahuda (Kiriyat Yeyarim) don su haura daga can su kawo akwatin alkawarin Allah Ubangiji, wanda yake zama tsakanin kerubobi, akwatin alkawarin da ake kira da Sunan.
7 And they set the ark of God upon a new cart, and brought it out of the house of Abinadab; and Uzza and Ahio drove the cart.
Suka ɗauki akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab a kan sabon keken shanu, Uzza da Ahiyo ne suke lura da shi.
8 And David and all Israel played before God with all their might; even with songs, and with harps, and with psalteries, and with timbrels, and with cymbals, and with trumpets.
Dawuda da dukan Isra’ilawa suka yi shagali da dukan ƙarfinsu a gaban Allah, tare da waƙoƙi da garayu, molaye, ganguna, kuge da ƙahoni.
9 And when they came unto the threshing-floor of Chidon, Uzza put forth his hand to hold the ark; for the oxen stumbled.
Sa’ad da suka kai masussukar Kidon, Uzza ya miƙa hannunsa don yă gyara akwatin alkawarin, gama shanun sun yi tuntuɓe.
10 And the anger of the LORD was kindled against Uzza, and He smote him, because he put forth his hand to the ark; and there he died before God.
Sai fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Uzza, ya kuma buge shi domin ya sa hannunsa a kan akwatin alkawarin. Sai ya mutu a can a gaban Allah.
11 And David was displeased, because the LORD had broken forth upon Uzza; and that place was called Perez-uzza unto this day.
Ran Dawuda ya ɓace domin Ubangiji ya husata a kan Uzza, kuma har wa yau ana ce da wannan wuri Ferez Uzza.
12 And David was afraid of God that day, saying: 'How shall I bring the ark of God home to me?'
Dawuda ya ji tsoron Allah a wannan rana ya kuma yi tambaya, “Yaya zan taɓa kawo akwatin alkawarin Allah gare ni?”
13 So David removed not the ark unto him into the city of David, but carried it aside into the house of Obed-edom the Gittite.
Don haka bai ɗauki akwatin alkawarin ya kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka, ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
14 And the ark of God remained with the family of Obed-edom in his house three months; and the LORD blessed the house of Obed-edom, and all that he had.
Akwatin Alkawarin Allah ya zauna tare da iyalin Obed-Edom a gidansa wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkaci gidan Obed-Edom da kome da yake da shi.

< 1 Chronicles 13 >