< Mark 13 >
1 AND as he was going out of the temple, one of his disciples said unto him, Master, behold what vast stones, and what structures!
da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
2 And Jesus answering said to him, Beholdest thou these magnificent structures? there shall not be left one stone upon another which shall not be thrown down.
Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
3 And as he was sitting on the mount of Olives, opposite the temple, Peter and James and John and Andrew asked him privately,
Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
4 Tell us, when shall these things be? and what is the sign when all these things shall come to pass?
Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
5 Then Jesus answering them, began to say, Beware that no man deceive you:
Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
6 for many will come in my name, saying, I am the Messiah; and shall deceive many.
Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7 But when ye hear of wars, and rumours of wars, be not troubled: for these things must be; but the end is not yet.
In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
8 And nation shall rise up against nation, and kingdom against kingdom: and there shall be earthquakes in divers places, and there shall be famines and commotions: these are the beginnings of sorrows.
Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9 But take ye heed to yourselves: for they shall deliver you up to their sanhedrims, and to the synagogues; ye shall be beaten with rods, and be set before kings and governors for my name’s sake, for a testimony unto them.
Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
10 And the Gospel must first be preached to all nations.
Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11 But when delivering you up, they shall bring you to the bar, be not previously anxious what ye shall say, neither premeditate: for it shall be given to you at that very hour, what ye shall speak: for it is not you, who are speaking, but the Holy Ghost.
Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
12 And brother shall deliver up brother unto death, and the father the son: and children shall rise up against their parents, and cause them to be put to death.
Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
13 And ye shall be hated of all men for my name’s sake. But he that endureth to the end, the same shall be saved.
Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14 But when ye see the abomination of desolation, spoken of by the prophet Daniel, standing where it ought not (let him that readeth observe), then let those who are in Judea fly to the mountains:
Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
15 and let not him who is on the roof go down into the house, nor enter into it, to carry away any thing out of the house:
Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
16 and he that is in the field, let him not return back to take his garment.
Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17 But wo to those who are big with child, and who have infants at their breasts in those days!
Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
18 And pray that your flight be not in winter.
Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
19 For these days shall bring tribulation, such as the like hath never been from the beginning of the creation which God created unto this time, and never shall be more.
A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
20 And except the Lord had shortened the days, no flesh would have been preserved: but for the sake of those elect, whom he hath elected, he hath shortened the days.
In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21 And then, if any man say to you, Lo, here is the Messiah! or, lo there! believe it not.
To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
22 For many false Messiahs and false prophets shall arise, and shall propose signs and wonders to deceive, if it were possible, even the elect.
Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
23 But be ye on your guard: lo! I have told you all things:
Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24 but in those days, after that distressing season, the sun shall be darkened, and the moon shall not emit her light;
Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
25 and the stars of the heaven will be falling, and the powers that are in heaven will be shaken.
Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
26 And then shall they see the Son of man coming in the clouds of heaven with vast power and glory.
Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
27 And then shall he send his angels, and shall gather to him his elect from the four winds, from the extremity of the earth to the utmost bound of heaven.
Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28 Now learn from the fig-tree, a parable; When her branch is now become tender, and putteth forth leaves, ye know that summer is nigh;
“Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
29 so also you, when ye see these things come to pass, know that it is nigh, even at the doors.
Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30 Verily I say unto you, That this generation shall not pass away, until all these things are fulfilled.
Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
31 Heaven and earth shall pass away; but my words shall never pass away.
Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
32 But of that day and hour knoweth no man, nor the angels which are in heaven, nor the Son, but the Father.
Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33 Take ye heed, watch, and pray; for ye know not when the time is.
Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
34 As a man going abroad, when he left his abode, and gave his servants authority, and to each his work, commanded also the porter to watch.
Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35 Watch ye therefore; for ye know not at what time the master of the house cometh, at evening, or midnight, or cock-crowing, or in the morning:
To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
36 lest coming suddenly he find you asleep.
Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
37 Now what I say to you, I say to all, Watch.
Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”