< Luke 3 >

1 NOW in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being governor of Judea, and Herod tetrarch of Galilee, and Philip his brother tetrarch of Iturea and the region of Trachonitis, and Lysanias tetrarch of Abilene:
A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
2 when Annas and Caiaphas were high-priests, the word of God came to John the son of Zacharias in the wilderness;
kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
3 and he came into all the country on the confines of Jordan, preaching the baptism of repentance for the remission of sins;
Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
4 as it is written in the book of the words of the prophet Isaiah, saying, “The voice of one crying in the wilderness, Prepare ye the way of the Lord, make his paths strait:
Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
5 every valley shall be filled up, and every mountain and hill shall be levelled, and the crooked ways made strait, and the rough roads smooth:
Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
6 and all flesh shall see the salvation of God.”
kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
7 He said, therefore, to the multitudes who came out to be baptised by him, Ye broods of vipers, who hath warned you to fly from the approaching wrath?
Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Produce then fruits worthy of repentance, and begin not to say in yourselves, We have a father, even Abraham; for I say unto you, That God is able out of these stones to raise up children to Abraham.
Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9 But now is the ax laid even to the root of the trees; every tree therefore that produceth not good fruit, is cut down and cast into the fire.
Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
10 And the multitudes asked him, saying, What then shall we do?
Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
11 And he answering said to them, He that hath two coats, let him give to him that hath none; and he that hath provisions, let him do in like manner.
Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
12 Then came also the farmers of the taxes to be baptised, and they said unto him, Master, what shall we do?
Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
13 He said unto them, Exact nothing more than is appointed for you.
Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
14 And the military men also asked him, And what shall we do? And he said unto them, Extort nothing by force; nor turn informers; and be content with your pay.
Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
15 Now when the people were in expectation, and many reasoned in their hearts respecting John, whether he were the Messiah,
Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
16 John addressed himself to them all, saying, I indeed baptise you with water; but one mightier than I is coming, the thong of whose sandals I am not worthy to untie: he shall baptise you with the Holy Ghost and with fire;
Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
17 whose winnowing fan is in his hand, and he will thoroughly cleanse his threshing-floor, and collect the wheat into his granary; but the chaff he will burn with fire unquenchable.
Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
18 Thus in many and various discourses exhorting them, he preached the glad tidings of the gospel to the people.
Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
19 Now Herod the tetrarch, being reproved by him, on account of Herodias his brother Philip’s wife, and for all the other wicked actions which he had done,
Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
20 added this also to all the rest, and shut up John in prison.
Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
21 Now it came to pass, at the time when John was baptising all the people, that Jesus also was baptised, and as he prayed, the heaven was opened,
Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
22 and the Holy Ghost descended in a bodily form, like a dove, upon him, and a voice came from heaven, saying, Thou art my beloved Son, in thee I am well pleased.
kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
23 And Jesus himself was about thirty years of age when he began his ministry, being (as was supposed the son of Joseph) of Heli,
Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
24 of Matthat, of Levi, of Melchi, of Janna, of Joseph,
dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
25 of Mattathias, of Amos, of Naum, of Esli, of Nagge,
dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
26 of Maath, of Mattathias, of Semei, of Joseph, of Juda,
dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
27 of Joanna, of Rhesa, of Zerubbabel, of Salathiel, of Neri,
dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
28 of Melchi, of Addi, of Cosam, of Elmodam, of Er,
dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
29 of Jose, of Eliezer, of Jorim, of Matthat, of Levi,
dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
30 of Simeon, of Judah, of Joseph, of Jonan, of Eliakim,
dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
31 of Melea, of Menan, of Mattatha, of Nathan, of David,
dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
32 of Jesse, of Obed, of Booz, of Salmon, of Naasson,
dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
33 of Aminadab, of Aram, of Esrom, of Phares, of Judah,
dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
34 of Jacob, of Isaac, of Abraham, of Terah, of Nachor,
dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
35 of Saruch, of Ragau, of Phalec, of Heber, of Sala,
dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
36 of Cainan, of Arphaxad, of Sem, of Noe, of Lamech,
dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
37 of Methusaleh, of Enoch, of Jared, of Maleleel, of Cainan,
dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
38 of Enos, of Seth, of Adam, the son of God.
dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.

< Luke 3 >